Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida Afrika
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana Afrika
  • GOSERC Ta NemI Haɗin Kan Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Inganta Wutar Lantarki A Gombe Afrika
  • Ranar Zaman Lafiya: Pastor Yohanna Buru Ya Jagoranci Tawagar Kiristoci Zuwa JNI Kaduna Afrika
  • Burkina Faso Ta Fara Kera Motocin Yaƙi Afrika

ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala
Published: September 20, 2026 at 11:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Daga Mohamman Awwal Garba a Kamaru

Ƙungiyar ANNOUR ta tallafa wa yara kusan 500 daga iyalai masu ƙaramin ƙarfi a birnin Douala na Kamaru, ta hanyar rabon kayan makaranta da kuɗinsu ya kai kimanin Francs CFA miliyan 5 da dubu 500.

An gudanar da shirin ne a filin waha na wasannin Olympics da ke Douala, domin taimaka wa iyalai wajen rage musu nauyin kuɗaɗen da ake kashewa wajen shirya yara zuwa sabon zangon karatu.

Taron ya gudana ƙarƙashin jagorancin El Hadj Aboubakar Bako Mandeng, Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiyar Musulmi ta yankunan Littoral da Kudu maso Yamma, tare da halartar wasu daga cikin sarakunan gargajiyar da ke cikin majalisar.

Ƙungiyar ANNOUR, ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba El Hadj Zakari Yaou, ta shafe shekaru shida tana gudanar da shirye-shiryen tallafawa al’umma, musamman mutanen da ke cikin mawuyacin hali.

Shirin tallafawa yaran bai tsaya a Douala kaɗai ba. A makon da ya gabata, ƙungiyar ta kai irin wannan tallafi yankin Penja, yayin da take shirin faɗaɗa ayyukan zuwa Moutenguéné da Tiko.

Ana sa ran cewa jimillar yara kusan 1,000 a waɗannan yankuna za su amfana da shirin.

Ƙungiyar ta ce ta himmatu wajen ci gaba da shirye-shiryen tallafawa masu ƙaramin ƙarfi, tare da ba da fifiko ga yara da iyalan da ke fuskantar matsalolin rayuwa.

Shirin ya samu yabo daga iyalan da suka amfana da tallafin, da kuma manyan baƙin da suka halarci taron a Douala, waɗanda suka bayyana shi a matsayin wani muhimmin mataki na tallafa wa ilimi da jin daɗin al’umma.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NEDC Ta Fara Shirin Kera Sanitary Pads A Gombe Domin Samar Da Sana’o’i Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ANNOUR Ta Raba Kayan Makaranta Na CFA Miliyan 5.5 Ga Yara A Douala
  • Ƙungiyoyin Fararen Hula Sun Ƙarfafa Yaƙi Da Gurɓacewar Muhalli A Kaduna
  • Sabbin Shugabannin NUJ Bauchi Sun Sha Alwashin Inganta Aikin Jarida
  • INEC Ta Ce Zaɓen Gombe, Kwami Da Funakaye Yana Gudana Cikin Lumana
  • Zaɓen Gombe: ’Yan Sanda Sun Sanar Da Tsauraran Matakan Tsaro Ranar Asabar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.