Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya.
Published: December 4, 2025 at 11:40 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 5, 2025

Kyaftin din Super Eagles William Troost-Ekong ya sanar da yin ritaya daga buga kwallon kafa na kasa da kasa.

Hakan yasa dan wasan mai shekaru 32 ba zai buga gasar cin kofin kasashen Afirka da ke tafe ba, wanda hakan shine ya kasance babban gasa ta farko da Najeriya za ta halarta ba tare da shi ba cikin kusan shekaru 10.

Troost-Ekong, wanda ya yi wasanni 83 kuma ya buga manyan gasa biyar, ya ce wannan shawarar ta zo ne da cikin kwanciyar hankali da sanin cewa a duk wadannan muhimman abubuwan da na yi na bayar da duk wata gudumawa da nake da shi.”

Da yake tunani game da tafiyarsa, ya ce sanya rigar babban kungiyar kwallon kafar Najeriya “ya fi buga kwallon kafa.

Tsohon kyaftin din Super Eagles ya bayyana wasansa na farko a shekarar 2015 a matsayin lokacin da komai ya canza, yana tunawa da yadda marigayi Stephen Keshi ya amince da shi tun da farko “in ji shi.

Troost-Ekong ya nuna jin dadi na damar da ya samu na jagorantar Najeriya, musamman a lokacin gasar AFCON ta 2023, inda aka nada shi Dan wasan Gasar bayan ya zura kwallo a wasan karshe.

“Wannan gasar ta koya min abin da ake nufi da zama dan Najeriya: muna fafatawa cikin wahala kuma muna kokari,” in ji shi.

Ya kuma yaba wa magoya baya da abokan wasansa wadanda suka tafiya tare ta tsawon shekaru goma.

An haife William a ƙasar Netherlands mahaifiyarsa ‘yar kasar Holland mahaifinsa dan Najeriya, maisuna Troost-Ekong ya wakilci Netherlands a matakin matasa kafin daga bisani ya sadaukar da kansa ga Najeriya.

Ya fara buga wasa a matakin farko a watan Yunin 2015 a wasan share fagen shiga gasar AFCON da Chad.

Kwallaye biyar da ya ci a gasar cin kofin kasashen Afirka sun kasance mafi yawan jimillar kwallaye da wani mai tsaron baya ya ci a tarihin gasar.

Troost-Ekong ya buga wasanin kwallon kafa a kasashen Turai, inda ya yi wasa a Ingila, Italiya, Turkiyya da Girka kafin ya koma PAOK a watan Yulin 2023.

A watan Agustan 2024, ya koma ƙungiyar Al-Kholood ta Saudiyya.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel
Next Post: Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
  • Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.