Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Published: December 7, 2025 at 4:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewar tana duba yuwuwar bude makarantu a farkon sabon shekara mai zuwa bayan hutun karshen shekara, yayin da take ci gaba da tantance yanayin tsaro a fadin jihar.

Majiyar mu ta habarto cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar Bauchi, Dr. Muhammad Lawal Rimin Zayam, ya ce akwai yuwuwar makarantu su koma karatu a farkon shekarar 2026 tare da shirya jarabawar zangon farko nan take bayan komawa.

A ranar 23 ga watan Nuwamba, na shekarar 2025 ne Ma’aikatar Ilimi ta bayar da umarnin rufe dukkannin makarantun jihar, har da manyan makarantu, sakamakon yawaitar sace sacen dalibai da ake fama da su a sassan kasa.

A cewar Kwamishinan, lokacin da aka rufe makarantun, saura kimanin makonni biyu ne a kammala zangon karatu da ake ciki.

Ya ce gwamnati za ta yi amfani da wannan damar wajen gudanar da gyar gyare a makaranti jihar domin samar da yanayi mai kyau da aminci ga dalibai lokacin da suka koma Makarantu domin kyautata ilimi.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin da ake yi na komawa makarantu ya yi daidai da shirinSafe Schools Initiative, inda ya kara da cewa yawancin makarantun jihar yanzu suna da katanga domin karfafa tsaro.

Ya kuma shawarci dalibai su ci gaba da karatu a lokacin hutun ta hanyar amfani da Fasahar zamani ta Nigeria e-learning platform, wato tsarin koyo da aka yi amfani da shi a lokacin kulle na COVID-19.

Kwamishinan ya kara da cewa dalibai za su ci gaba da zangon karatu ba tare da wani hutun karshen zangon ba, domin cike gibin lokacin da aka rasa yayin rufe makarantun.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Next Post: Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Amurka Ta Girke Jirage Marasa Matuki Tare Da Sojoji A Najeriya Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.