Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: December 9, 2025 at 7:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 9, 2025

Burkina Faso ta tsare sojojin Najeriya 11, ta kuma kwace jirgin saman NAF saboda shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin sojin Burkina Fason ce, ta tabbatar da tsare jami’an sojan Najeriya 11 tare da kwace wani jirgin dakon kaya na rundunar sojin saman Najeriya (NAF) bayan ya shiga sararin samaniyar kasar ba tare da izini ba sannan ya yi saukar gaggawa.

A cikin sanarwar da Kungiyar Kasashen Sahel (Alliance of Sahel States – AES) ta fitar a daren Litinin, an ce jirgin C-130 na sojin saman Najeriya ya yi saukar gaggawa a Bobo Dioulasso a ranar 8 ga Disamba, 2025, sakamakon matsalar fasaha yayin da yake shawagi a cikin sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izinin shiga ba.

AES dai ƙungiya ce da ta ƙunshi Burkina Faso, Nijar da Mali, dukkaninsu kuma suna ƙarƙashin mulkin soja.

Hukumomin kasar sun bayyana cewa jirgin na ɗauke da matuka biyu da kuma fasinjoji tara  dukkansu jami’an sojan Najeriya ne, ana tsare da su a halin yanzu a hannun hukumomin Burkina Faso.

Kungiyar AES ta yi Allah wadai da lamarin, tana mai cewa hakan babban take hakkin kasa da tauye ikon mallakar sararin samaniya ne amma kuma an kaddamar da cikakken bincike domin gano hakikanin dalilin shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

A martaninsu, AES ta sanar da cewa dakarun kasashen uku sun shiga matakin tsaro mafi girma ne, haka kuma, an bai wa rundunonin tsaro izinin amfani da makaman kare sararin samaniya da na harbo jiragen da zasu karya dokokin sararin samaniyar su.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato
Next Post: Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025:

Karin Labarai Masu Alaka

Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC Siyasa
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.