Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda
Published: December 11, 2025 at 1:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojojin Najeriya ta yi gagarumar nasara a kan tawagar Bello Turji bayan ta halaka babban kwamandan ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samame da ta kai a Sabon Birni, dake Jihar Sokoto.

Majiyar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun Runduna ta 8 tare da haɗin gwiwar ‘yan sakai sun gudanar da aikin ne a safiyar ranar Litinin a kauyen Kurawa, inda suka kuma kashe wani babban mai kai wa Turji kayayyakin aiki.

Kallamu, ɗan asalin Garin Idi a Sabon Birni, ya dade yana addabar yankin da hare hare, garkuwa da mutane da kuma harin gonaki sannan ya koma yankin bayan ya tsere daga wani samamen soji a Yuni 2025.

Masani kan tsaro, Prof. Murtala Ahmed Rufa’i, ya bayyana Kallamu a matsayin Buzu (Tuareg) wanda iyayensa suka shigo daga Nijar cikin 1972, yana jagorantar kusan mutane 100, da ke aikata ta’addanci a Isa, Sabon Birni, Shinkafi, Goronyo, har ma da wasu yankuna na Zamfara da Nijar.

Dogon Zango shi ne yankin da ya fi karfi, inda yake tsara hare-hare kan kauyuka da dama sannan ya kuma kasance cikin wadanda suka kai mummunan harin watan Disamba 2021, lokacin da aka ƙona matafiya bisa umarnin Turji.

Rufa’i ya ce mutuwarsa da ta mataimakinsa Halliru ta haifar da rikicewa a cikin tsarin Turji, yana mai cewa yanzu ne lokacin da sojoji za su iya cakuɗa sansanin Dogon Zango kafin su nada sabon shugaba.

Sai dai ya yi gargadin cewa ba lallai rasuwar Kallamu ta yi tasiri sosai a kan manyan ayyukan Turji ba, domin bai kasance cikin sahun manyan kwamandojinsa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC
Next Post: Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika
‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.