Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita
Published: December 16, 2025 at 4:11 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Buhari har kulle dakinsa ya dinga yi saboda ya yadda da jita-jitar cewa zan kashe shi  Inji Aisha Buhari

Aisha Buhari, matar marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ta ce mijinta ya fara kulle ɗakinsa bayan jita-jitar da ta bazu a Aso Rock cewa tana shirin kashe shi.

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce Buhari ya yarda da abin da ake yadawa, lamarin da ya sa ya sauya wasu daga cikin halayensa.

Aisha ta bayyana ƙwarewarta wajen kula da matsalolin lafiyar Buhari a cikin wani littafin tarihin rayuwarsa mai shafuka 600 mai taken “From Soldier to Statesman: The Legacy of Muhammadu Buhari” (Daga Soja zuwa Jagoran Ƙasa: Tarihin Muhammadu Buhari).

A cikin littafin, Aisha ta ce matsalar lafiyar da Buhari ya fuskanta a shekarar 2017 ba wata cuta ce mai ban mamaki ba ko sakamakon guba, sai dai ta fara ne bayan rushewar tsarin cin abinci da kuma rashin kula da tsarin gina jiki yadda ya kamata.

Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce tun da dadewa ita ke kula da abincin mijinta a wasu lokuta na musamman, tana mai cewa tsarin ya taimaka wa Buhari wajen kiyaye daidaiton lafiyarsa.

“A cewar Aisha Buhari, matsalar lafiyar mijinta a shekarar 2017 ba ta samo asali daga wata cuta mai ban mamaki ko makirci na ɓoye ba amma ta fara ne da lalacewar tsarin rayuwa; abin da ta kira ‘tsarin abincina’ wato tsarin cin abinci da ƙarin gina jiki da ta dade tana kula da su a Kaduna kafin su koma Aso Villa,” in ji littafin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje
Next Post: Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
Anyi Asarar Biliyoyin Naira A Gobarar Kasuwar Singa Labarai
Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.