Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela
Published: December 17, 2025 at 4:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Trump na Amurka ya bada umurnin a tare dukkan jiragen ruwan dakon mai da aka sanya ma takunkumi a hana su shiga Venezuela, a wani matakin da ake dauka a zaman karin matsin lamba a kan shugaba Nicolas Maduro da kuma takura tattalin arzikin kasar.

Wannan umurni na shugaba Trump yana zuwa a bayan da sojojin Amurka suka kama wani jirgin ruwan jigilar man fetur a makon da ya shige a kusa da gabar kasar Venezuela, a bayan da Amurka ta girka sojoji masu yawa a yankin.

A cikin bayanin da yayi a shafinsa na sada zumunta ranar talata, shugaba Trump yayi zargin cewa Venezuela tana amfani da kudin mai wajen karfafa safarar muggan kwayoyi da wasu laifuffukan, yana mai lasar takobin ci gaba da matsin lambar soja har sai kasar Venezuela ta mayar ma Amurka a cewarsa Mai da kasa da kuma kadarorinta.

Abinda ba a fahimta a wannan bayani na shugaban ba shine wane irin hakki Amurka take da shi a game da man fetur ko kasa ko kuma kadara na Venezuela.

Shugaba Nicolas Maduro ya yaba ma ‘yan kasarsa da yace an shafe makonni 25 ana neman firgita su da nuna musu yatsa.

Trump yace duk wannan matsin da ake yi na neman hana safarar muggan kwayoyi zuwa Amurka ne, amma kuma shugabar ma’aikatan sa Susie Wiles ta fada cikin wata hirar da aka wallafa ranar talata a mujallar Vanity cewa wannan matsi wani yunkuri ne na kawar da shugaba Maduro daga kan mulki.

Kasar venezuela ta fi kowace kasa a duniya arzikin man fetur.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba
Next Post: Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.