Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Published: December 19, 2025 at 5:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 19, 2025

Shugaban Najeriya Bola Tinubu a ranar Alhamis ya ƙara jaddada ƙudurin sa na kafa ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa ya ba wa Amurka da abokan hulɗan Turai tabbacin cewa zai aiwatar da tsarin ’yan sandan jihohi a Najeriya.

Ya jaddada cewa dole ne a kafa ’yan sandan jihohi “ba tare da ja da baya ba” a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsaron cikin gida da ƙarfafa tsarin mulki a matakin jihohi.

Tinubu ya faɗi hakan ne a taron ƙungiyar manyan jiga-jigan APC karo na 14 da aka gudanar a Cibiyar Taron Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

A wajen taron, ya kuma dage cewa ’dole ne aiwatar da hukuncin cin gashin kan Kananan hukumomi a aikace, inda ya buƙaci gwamnonin jihohi da su daina riƙe kuɗaɗen da aka ware wa shugabannin ƙananan hukumomi.

Jawaban Shugaban Ƙasa sun zo ne a daidai lokacin da matsalolin tsaro ke ƙaruwa a faɗin ƙasar, tare da sabbin kiraye-kirayen neman kafa’yan sandan Jihohi, da kuma ƙoƙarin aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi da kuma raba musu kuɗi kai tsaye.

Tinubu ya shawarci shugabannin jam’iyya cewa APC, a matsayin ta na jam’iyya mai rinjaye, dole ne ta nuna jagoranci ta hanyar sasantawa, fahimtar juna da sassauci a matakin ƙasa, yana kuma ƙarfafa gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin abin da ke faruwa a jihohin su da ƙananan hukumomin su.

Ya ce kwanan nan ya tattauna da abokan hulɗa na ƙasashen waje, inda ya tabbatar musu da cewa Najeriya za ta tunkari tsarin ’yan sandan jihohi, yana mai ƙarawa da cewa yana da tabbacin jam’iyyar APC za ta bayar da cikakken goyon baya.

Yakara da cewa,“Na yi doguwar tattaunawa da su abokan hulɗa daga Amurka da Tura kuma na faɗa musu cikin alfahari cewa tabbas za mu zantas da dokar ’yan sandan jihohi domin inganta tsaro.”

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya
Next Post: Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai
  • Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.