Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Published: December 22, 2025 at 9:09 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar litinin tsohon fira ministan kasar Malaysia, Najib Razak, zai san ko zai iya karasa sauran hukuncin daurin da aka yanke masa a gidansa, ko kuma a cikin kurkuku.

An yanke ma Razak hukuncin daurin shekaru 12 a gidan kurkuku a shekarar 2022, bisa laifin zarmiya da cin hanci a badakalar da aka fi sani da sunan abin Fallasa na 1MDB.

A shekarar da ta shige, wata hukumar yahudawa dake karkashin jagorancin tsohon Sarkin Malaysia, ta rage masa hukumcin zuwa shekaru 6.

Amma Razak ya ce Sarkin na Malaysia ya kuma bada umurnin cewa yana iya karasa wannan hukuncin a gidansa, watau daurin talala, kuma abinda ya sa ya shigar da kara ke nan a kotu yana neman a yi aiki da wannan umurnin da gwamnatin fira minista Anwar Ibrahim ta ce ba ta san da shi ba.

Jami’an gwamnati sunyi wata da watanni suna cewa ba su da wata masaniya game da wannan takardar umurni, duk da cewa a cikin wannan shekara, ofishin tsohon sarkin da ma wani lauya na tarayya sun gaskata cewa lallai an bayar da takardar umurnin rege hukumcin zuwa shekaru 6, kuma za a iya kyale ya karasa a gidansa.

Ranar litinin, babbar kotun birnin Kuala Lumpur zata yanke hukumci a kan wannan, kwanaki hudu kafin ta yanke hukunci a kan shari’a mafi girma da shi Najib yake fuskanta dangane da wannan abin fallasa na asusun 1Malaysia Development Berhad, wanda asusu ne na kudin gwamnati da ya taimaka wajen kirkirowa a shekarar 2009.

Masu fashin baki suka ce mutane ba zasu yi murna ba, musamman magoya bayan fira minista Anwar, idan kotun ta wanke shi a wancan zargin, Anwar dai ya ci zabe ne bisa alkawarin yaki da cin hanci da rashawa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine
Next Post: Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Real Madrid Ta Sauya Tsarin Gabatar Da Mourinho Da Sabbin ’Yan Wasanta A Santiago Bernabéu Wasanni
  • Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
  • Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.