Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Published: December 22, 2025 at 9:09 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar litinin tsohon fira ministan kasar Malaysia, Najib Razak, zai san ko zai iya karasa sauran hukuncin daurin da aka yanke masa a gidansa, ko kuma a cikin kurkuku.

An yanke ma Razak hukuncin daurin shekaru 12 a gidan kurkuku a shekarar 2022, bisa laifin zarmiya da cin hanci a badakalar da aka fi sani da sunan abin Fallasa na 1MDB.

A shekarar da ta shige, wata hukumar yahudawa dake karkashin jagorancin tsohon Sarkin Malaysia, ta rage masa hukumcin zuwa shekaru 6.

Amma Razak ya ce Sarkin na Malaysia ya kuma bada umurnin cewa yana iya karasa wannan hukuncin a gidansa, watau daurin talala, kuma abinda ya sa ya shigar da kara ke nan a kotu yana neman a yi aiki da wannan umurnin da gwamnatin fira minista Anwar Ibrahim ta ce ba ta san da shi ba.

Jami’an gwamnati sunyi wata da watanni suna cewa ba su da wata masaniya game da wannan takardar umurni, duk da cewa a cikin wannan shekara, ofishin tsohon sarkin da ma wani lauya na tarayya sun gaskata cewa lallai an bayar da takardar umurnin rege hukumcin zuwa shekaru 6, kuma za a iya kyale ya karasa a gidansa.

Ranar litinin, babbar kotun birnin Kuala Lumpur zata yanke hukumci a kan wannan, kwanaki hudu kafin ta yanke hukunci a kan shari’a mafi girma da shi Najib yake fuskanta dangane da wannan abin fallasa na asusun 1Malaysia Development Berhad, wanda asusu ne na kudin gwamnati da ya taimaka wajen kirkirowa a shekarar 2009.

Masu fashin baki suka ce mutane ba zasu yi murna ba, musamman magoya bayan fira minista Anwar, idan kotun ta wanke shi a wancan zargin, Anwar dai ya ci zabe ne bisa alkawarin yaki da cin hanci da rashawa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine
Next Post: Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia

Karin Labarai Masu Alaka

Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika
Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli Afrika
UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.