Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta cika alkawarin da tayi na bai wa ‘yan wasan Super Eagles Gidajen bayan kammala Gasar AFCON 2023.
‘Yan wasan tawagar Ƙungiyar Kwallon kafar Super Eagles na Najeriya sun karbi Gidajen da Gwamnatin Ƙasar ta yi musu alkawari sakamakon nasarar da suka samu a Gasar cin kofin Kasashen Afirka na 2023 (AFCON) wacce Ƙasar Côte d’Ivoire ta karbi bakunci.

Inda Super Eagles ta kare a matsayi na biyu an gabatar wa ‘Yan Wasan, takardun mallakar Gidaje da kuma raba musu filaye a Matsayin wani kyautata da kuma karfafa musu gwiwa kamar yadda Gwamnatin Tarayya ta yi alkawarin yin hakan tun wacan shekarar.
Gwamnatin ta gabatar da wannan Kyauta ne kafin Shirye-shiryen Najeriya na gasar AFCON da akeyi bana wadda hakan ya zama kara masu kwarin gwiwa da kuma zaburar da Kungiyar yayin da suke wakiltar Ƙasar a gasar na Nahiyar Ƙasashen afirka 2025, wace ke gudana a ƙasar Moroko.

Wannan cika alkawarin gidaje, da Gwamnatin Tarayya ta yi wa ƙwararrun, wani mataki da masu ruwa da tsaki ke ganin zai iya ƙara ƙarfafa wa ‘yan wasa da ke wakiltar ƙasar a gasannin daban-daban na ƙasa da ƙasa.
ƙungiyar Super Eagles a Yau zasu fafata da ƙasar Tanzaniya a wasan ta


