Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya
Published: December 24, 2025 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Babban hafsan hafsoshin sojan kasar Libya, Mohammed Ali Ahmed al-Haddad, ya mutu a lokacin da jirgin saman da yake ciki yayi hatsari bayan tashin sa daga Ankara, babban birnin Turkiyya ranar talata da maraice.

Fira ministan gwamnatin kasar Libya wadda kasashen duniya suka amince da ita, Abdulhamid Dbeibah, ya fada cikin wata sanarwa cewa akwai wasu jami’an gwamnatin ta Libya su hudu a cikin wannan jirgi.

Fira ministan yace wannan lamari ya faru ne a lokacin da babban hafsan tare da tawagarsa suke komawa gida a bayan ziyarar aiki a babban birnin na Turkiyya.

Yace sauran wadanda suke cikin wannan jirgi sun hada da kwamandan rundunar sojojin kasar ta Libya, da daraktan hukumar kere-keren kayan soja, da wani mai bawa babban hafsan shawara tare da wani mai daukar hoto daga ofishinsa.

Ministan harkokin cikin gidan Turkiyya, Ali Yerlikaya ya fada a shafin sada zumunci na X cewa jirgin ya tashi a kan hanyar komawa Tripoli daga filin jirgin saman Esenboga na Ankara da karfe 5 da minti 10 na yamma agogon kasar, kuma ya bace da karfe 5 da minti 52. Ya ce hukumomi sun gano inda jirgin ya fadi a gundumar Haymana ta lardin Ankara.

Yace wannan jirgi kirar Dassault Falcon-50, ya nemi a ba shi iznin saukar gaggawa a lokacin da yake wucewa ta samaniyar Haymana, amma sai aka kasa samunsa ta rediyo.

Ba a san abinda ya haddasa faduwar jirgin ba, amma Ministan shari’a na Turkiyya, Yilmaz Tunc, yace an kaddamar da bincike.

Wani karamin ministan harkokin siyasa da sadarwa a gwamnatin hadin kan kasa ta Libya, Walid Ellafi, ya fadawa kafar sadarwar Al-Ahrar ta libya cewa jirgin na haya ne daga wani kamfani a kasar Malta sannan yace jami’ai ba su da cikakken bayani a game da tarihin wannan jirgi ko wanda ya mallake shi, amma dai abu ne da zai fito a binciken da aka kaddamar.

Gwamnatin kasar wadda ita ce kadai MDD ta amince da ita a zaman hukuma a kasar libya, ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku a kasar.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Next Post: Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta

Karin Labarai Masu Alaka

Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar Tsaro
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.