Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe
Published: December 27, 2025 at 1:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Mummunan hatsari yayi Ajalin Mutane bakwai a jihar Gombe, yayinda Gwamna Inuwa Yahaya Ya Miƙa Ta’aziyya Ga Al’ummar Lawanti Sakamakon Wannan Hatsari

Rahotanni sun ce waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu ta zuwa Maiduguri babban birnin jihar Borno, don halartar wani bikin aure.

An bayyana sunayen mamatan kamar haka, Gambo Abbo, mai shekara 35, Umalkhairi, mai shekara 18, Rabiu Abubakar, mai shekara 28, Fatuma Hassan, mai shekara 28, Amal Abubakar, mai shekara 3 Adamu Bello, mai shekara 4 da Zarau Alhaji, mai shekara 27.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan labari, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da ban tsoro, ba kawai ga iyalan da abin ya shafa ba, har ma ga dukkan al’ummar Lawanti, Ƙaramar Hukumar Akko da kuma jihar Gombe baki ɗaya.

Yace mutuwar kwatsam ta irin waɗannan mutane masu tasiri ta taɓa zuƙatan kowa, yana mai cewa babu wata kalma da za ta iya ta’azantar da iyalan waɗanda suka rasa ƙaunatattunsu a cikin irin wannan yanayi mai ban tausayi.

Gwamnan ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, musamman Hakimin Jalingo, Bello Hassan Babangida wanda ya rasa ‘yar uwarsa da kuma yayansa da Idris Lawanti Maigari, wanda ya rasa ‘yarsa da Kansila mai wakiltar Gundumar Akko, Idris A. Isah Lawanti, wanda shi ma ya rasa ‘yan uwa na kurkusa.

Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya baiwa iyalan da suka rasu, da ƴan uwa da kuma duk al’ummar Lawanti yayi fatan su zamo masu juriya, haƙuri da ƙarfin halin ɗaukar wannan babban rashi, sannan kuma Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu da rahamarsa.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa mamatan abyafe kurakuransu, ya karɓi kyawawan ayyukansu ya kuma saka musu da Aljannatul Firdausi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.