Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe
Published: December 27, 2025 at 1:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Mummunan hatsari yayi Ajalin Mutane bakwai a jihar Gombe, yayinda Gwamna Inuwa Yahaya Ya Miƙa Ta’aziyya Ga Al’ummar Lawanti Sakamakon Wannan Hatsari

Rahotanni sun ce waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu ta zuwa Maiduguri babban birnin jihar Borno, don halartar wani bikin aure.

An bayyana sunayen mamatan kamar haka, Gambo Abbo, mai shekara 35, Umalkhairi, mai shekara 18, Rabiu Abubakar, mai shekara 28, Fatuma Hassan, mai shekara 28, Amal Abubakar, mai shekara 3 Adamu Bello, mai shekara 4 da Zarau Alhaji, mai shekara 27.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan labari, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da ban tsoro, ba kawai ga iyalan da abin ya shafa ba, har ma ga dukkan al’ummar Lawanti, Ƙaramar Hukumar Akko da kuma jihar Gombe baki ɗaya.

Yace mutuwar kwatsam ta irin waɗannan mutane masu tasiri ta taɓa zuƙatan kowa, yana mai cewa babu wata kalma da za ta iya ta’azantar da iyalan waɗanda suka rasa ƙaunatattunsu a cikin irin wannan yanayi mai ban tausayi.

Gwamnan ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, musamman Hakimin Jalingo, Bello Hassan Babangida wanda ya rasa ‘yar uwarsa da kuma yayansa da Idris Lawanti Maigari, wanda ya rasa ‘yarsa da Kansila mai wakiltar Gundumar Akko, Idris A. Isah Lawanti, wanda shi ma ya rasa ‘yan uwa na kurkusa.

Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya baiwa iyalan da suka rasu, da ƴan uwa da kuma duk al’ummar Lawanti yayi fatan su zamo masu juriya, haƙuri da ƙarfin halin ɗaukar wannan babban rashi, sannan kuma Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu da rahamarsa.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa mamatan abyafe kurakuransu, ya karɓi kyawawan ayyukansu ya kuma saka musu da Aljannatul Firdausi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Anyi Asarar Biliyoyin Naira A Gobarar Kasuwar Singa Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.