Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe
Published: December 27, 2025 at 1:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Mummunan hatsari yayi Ajalin Mutane bakwai a jihar Gombe, yayinda Gwamna Inuwa Yahaya Ya Miƙa Ta’aziyya Ga Al’ummar Lawanti Sakamakon Wannan Hatsari

Rahotanni sun ce waɗanda abin ya shafa suna kan hanyarsu ta zuwa Maiduguri babban birnin jihar Borno, don halartar wani bikin aure.

An bayyana sunayen mamatan kamar haka, Gambo Abbo, mai shekara 35, Umalkhairi, mai shekara 18, Rabiu Abubakar, mai shekara 28, Fatuma Hassan, mai shekara 28, Amal Abubakar, mai shekara 3 Adamu Bello, mai shekara 4 da Zarau Alhaji, mai shekara 27.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan labari, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana lamarin a matsayin babban rashi mai raɗaɗi da ban tsoro, ba kawai ga iyalan da abin ya shafa ba, har ma ga dukkan al’ummar Lawanti, Ƙaramar Hukumar Akko da kuma jihar Gombe baki ɗaya.

Yace mutuwar kwatsam ta irin waɗannan mutane masu tasiri ta taɓa zuƙatan kowa, yana mai cewa babu wata kalma da za ta iya ta’azantar da iyalan waɗanda suka rasa ƙaunatattunsu a cikin irin wannan yanayi mai ban tausayi.

Gwamnan ya jajantawa iyalan waɗanda abin ya shafa, musamman Hakimin Jalingo, Bello Hassan Babangida wanda ya rasa ‘yar uwarsa da kuma yayansa da Idris Lawanti Maigari, wanda ya rasa ‘yarsa da Kansila mai wakiltar Gundumar Akko, Idris A. Isah Lawanti, wanda shi ma ya rasa ‘yan uwa na kurkusa.

Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya baiwa iyalan da suka rasu, da ƴan uwa da kuma duk al’ummar Lawanti yayi fatan su zamo masu juriya, haƙuri da ƙarfin halin ɗaukar wannan babban rashi, sannan kuma Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu da rahamarsa.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah ya gafartawa mamatan abyafe kurakuransu, ya karɓi kyawawan ayyukansu ya kuma saka musu da Aljannatul Firdausi.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji

Karin Labarai Masu Alaka

Hadakar Kungiyoyin Sauyin Yanayi Ta Bukaci ‘Yan Siyasa Su Dauki Matakan Kare Muhalli Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika
Yusuf Gawuna Ya Koma Jam’iyar ADC Afrika
Mace Ta Farko Da Zata Shugabanci Jami’ar Northwest Dake Kano Najeriya
Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel Afrika
Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
  • Da Alamu Ronaldo Zai Buga Dukkan Wasanni Da Gasar Kofin Duniya A 2026 Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi Tsaro
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.