Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Published: December 27, 2025 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya tace harin da Amurka ta kai ta sama wadda take goyon bayansa matakin ya afkawa sansanonin ‘yan bindigar ISIS guda biyu a dajin da ake kira Bauni dake jihar Sokoto, inda ta auna mayaka daga ketare wanda suke shiga Najeriya daga yankin Sahel.

Farmakin da aka kai ranar Alhamis, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince dashi, wadda aka kaddamar daga sasanonin Amurka na ruwa daga gabar da teku da ake kira Gulf a Guniea, bayan wani lokaci mai tsawo ana tattara bayanan sirri, da tsare tsare, kamar yadda ma’aikatar yada labarai ta Najeriya ta bada sanarwa a ranar jumma’a.

Adadin makamai 16 masu aiki da GPS aka yi amfani da su, wadda suka yi nasarar gamawa da mayakan ISIS wadanda suke kokarin kutsawa cikin Najeriya daga yankin na Sahel, inji hukumomin Najeriya.

Bayanan sirri sun nuna cewa, mayakan kungiyar ISIS daga waje ne suke amfani da sansanoni tare da hadin guiwar wasu kungiyoyin mayaka daga cikin gida inda suke shirya kai munanan hare hare, kamar yadda sanarwar tayi karin bayani.

Ta kara da cewa harin bai rutsa da farar hula ba, koda shike baragusai sun fada kan wasu garuruwa a jihohin Sokoto da kwara.

Farmakin da Amurkan ta kai ya nuna hadin kan tsaro na ba sabon ba tsakanin hukumomi a Abuja da Washington, ganin yadda tashe-tashen hankula da ake alakantawa da addinin Musulunci suke kara bazuwa zuwa a kudanci daga yankin Sahel.

Gwamnatin Najeriya tace a shirye take ta ci gaba da daukar matakai na kare rayuka da dukiyoyin al’umarta, yayinda shugaba Trump na Amurka yace a shirye Washington take ta kai karin wasu hare hare.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji
Next Post: Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 30 A Jihar Neja Najeriya
Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai
Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.