Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Published: December 27, 2025 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya tace harin da Amurka ta kai ta sama wadda take goyon bayansa matakin ya afkawa sansanonin ‘yan bindigar ISIS guda biyu a dajin da ake kira Bauni dake jihar Sokoto, inda ta auna mayaka daga ketare wanda suke shiga Najeriya daga yankin Sahel.

Farmakin da aka kai ranar Alhamis, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince dashi, wadda aka kaddamar daga sasanonin Amurka na ruwa daga gabar da teku da ake kira Gulf a Guniea, bayan wani lokaci mai tsawo ana tattara bayanan sirri, da tsare tsare, kamar yadda ma’aikatar yada labarai ta Najeriya ta bada sanarwa a ranar jumma’a.

Adadin makamai 16 masu aiki da GPS aka yi amfani da su, wadda suka yi nasarar gamawa da mayakan ISIS wadanda suke kokarin kutsawa cikin Najeriya daga yankin na Sahel, inji hukumomin Najeriya.

Bayanan sirri sun nuna cewa, mayakan kungiyar ISIS daga waje ne suke amfani da sansanoni tare da hadin guiwar wasu kungiyoyin mayaka daga cikin gida inda suke shirya kai munanan hare hare, kamar yadda sanarwar tayi karin bayani.

Ta kara da cewa harin bai rutsa da farar hula ba, koda shike baragusai sun fada kan wasu garuruwa a jihohin Sokoto da kwara.

Farmakin da Amurkan ta kai ya nuna hadin kan tsaro na ba sabon ba tsakanin hukumomi a Abuja da Washington, ganin yadda tashe-tashen hankula da ake alakantawa da addinin Musulunci suke kara bazuwa zuwa a kudanci daga yankin Sahel.

Gwamnatin Najeriya tace a shirye take ta ci gaba da daukar matakai na kare rayuka da dukiyoyin al’umarta, yayinda shugaba Trump na Amurka yace a shirye Washington take ta kai karin wasu hare hare.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji
Next Post: Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
Azumin Ramadan Yahadu Da Azumin Lent Da Mabiya Addinin Kirista Sukeyi A Wannan Shekarar Labarai
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu Afrika
  • ’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.