Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware
Published: December 27, 2025 at 9:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar hadin kai da Saudiyya take yiwa jagoranci a Yemen tace zata maida martani kan duk wani yunkurin da ‘yan aware dake kudancin lardin Hadaramount suka yi, wadda ka iya illa ga kokarin tsagaita wuta kamar yadda Kamfanin dilancin labarai na Saudiyya ya bayyana a yau Asabar.

Sanarwar da kakakin rundunar hadin guiwa Janar Turki al-Maliki ya bayar, ya biyo bayan bukatar da shugaban majalisar gudanarwa a Yemen,Rashad al-Alimi yayi na daukar matakan gaggawa domin kare farar hula a lardin Hadaramount bayanda mayaka wadanda suke da alaka da kungiyar ‘yan tawaye da ake yiwa lakabi da STC suka keta yarjejenyar da take aiki na tsagaita wuta

Kungiyar ‘yan tawayen STC watau Southern Transitional Council da turanci, wacce hadaddiyar daular larabawa take marawa baya, ta hambare gwamnatin yankin da Saudiyya da kuma kasashen duniya suka amince data ita a farkon watan nan daga helkwatarta dake Aden, kuma ta ayyana iko a duk fadin kudancin kasar.

A ranar Jumma’a dai kunigyar ta STC tayi watsi da kiran da Saudiyya tayi mata cewa ta janye daga sassan data kama a farkon watan nan, tana mai cewa zata ci gaba da aikin mamaye lardunan dake kudancin Yemen da ake kira Hadaramount da Mahra.

Daga bisani anji ministan tsaron Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, ta wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, yana kira ga Kungiyar ta STC ta saurari kokarin sulhu da ake yi, kuma ta amince da a gudanar da shawarwari da nufin shawo kan rikici a yankin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Next Post: Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika
Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
  • Gwamnatin Tinubu Ta Warware Basussukan Fansho Na Shekaru 18 Afrika
  • Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
  • Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.