Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Takaddama Ta Barke Tsakanin Lebanon Da Isra’ila Akan Bakin Iyaka
Published: November 16, 2025 at 12:52 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Lebanon ta ce zata kai karar Isra’ila gaban Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, a saboda wata katangar da ta gina ta kankare a bakin iyakar kudancin Lebanon, wadda ta tsallake bakin iyakar da majalisar ta shata dake raba tsakanin kasashen biyu.

Wannan iyakar da ake yi ma lakabi da Shudin Layi, MDD ce ta tsara shi domin raba tsakanin Lebanon da Isra’ila, da kuma Tuddan Golan na kasar Sham wadanda Isra’ila ta mamaye. Sojojin Isra’ila sun ja, suka koma bayan wannan layin a shekarar 2000 lokacin da suka janye daga kudancin Lebanon.

Wani kakakin babban sakataren MDD, Stephane Dujarric, yace wannan katanga ta Isra’ila ta sa wasu ‘yan kasar Lebanon ba su iya shiga wasu sassan yankunansu ba.

Ofishin shugaban Lebanon ya nanata wannan a lokacin da yake ci gaba da gina wannan katanga da Isra’ila keyi ya sabawa kuduri na 1701 na Kwamitin Sulhun MDD kuma ya keta haddin diyaucin kasar Lebanon,

A ranar Jumma’a, wani kakakin rundunar sojojin bani Isra’ila, ya musanta cewa wannan katanga da ake ginawa ta tsallake wannan layi da aka shata na iyaka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza
Next Post: Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.