Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina
Published: January 4, 2026 at 2:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojan Najeriya ta ce jiragen yaƙinta sun hallaka akalla ’yan bindiga 23 da ke tserewa daga jihar Kano zuwa jihar Katsina, a wani samame na haɗin gwiwa karkashin Operation Fansan Yamma.

A cewar rundunar, samamen ya biyo bayan wani hari da ake zargin ’yan bindiga sun kai a daren 1 zuwa safiyar 2 ga Janairu, 2026, a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa na Jihar Kano.

Dakarun haɗin gwiwa da ke Kano sun dakile harin cikin gaggawa tare da yi wa ’yan ta’addan mummunar ɓarna, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa jihar Katsina, Sojojin sun bi sahunsu har zuwa ƙauyen Karaɗuwa da ke Ƙaramar Hukumar Matazu.

A wata sanarwa da Mai Taimaka wa Daraktan Hulɗa da Jama’a na Birgediya na 3, Major Babatunde Zubairu, ya fitar, ya ce bayanan leƙen asiri sun nuna cewa ’yan bindigar suna gudanar da jana’izar abokansu da aka kashe a yankin Ɗan Marke, a Ƙaramar Hukumar Matazu, lokacin da dakarun sama suka ga motsinsu.

Sanarwar ta ce an ci gaba da bibiyar su har sai da suka haɗu da baburansu bayan sun ƙetare wani busasshen kwarin rafi, inda jiragen yaƙin sama suka kai musu luguden wuta.

Rundunar ta bayyana cewa an hallaka akalla ’yan ta’adda 23, yayin da ake kyautata zaton wasu da dama sun samu raunuka kuma harin ya kuma lalata makamai da kayan aiki da dama na ’yan bindigar.

Kwamandan Birgediya na 3 ya yaba da jarumtaka da jajircewar dakarun sama da na ƙasa, yana mai cewa sun nuna bajinta na musamman a fagen yaƙi.

Rundunar Soja ta tabbatar wa al’ummar jihar Kano cewa yankin na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali, tare da ci gaba da sintiri da sa ido a kai a kai.

Ta kuma gode wa jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa a yaƙi da ’yan ta’adda, tare da kiran su da su ci gaba da samar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile ayyukan ta’addanci.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba
Next Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika
Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.