Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina
Published: January 4, 2026 at 2:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar Sojan Najeriya ta ce jiragen yaƙinta sun hallaka akalla ’yan bindiga 23 da ke tserewa daga jihar Kano zuwa jihar Katsina, a wani samame na haɗin gwiwa karkashin Operation Fansan Yamma.

A cewar rundunar, samamen ya biyo bayan wani hari da ake zargin ’yan bindiga sun kai a daren 1 zuwa safiyar 2 ga Janairu, 2026, a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa na Jihar Kano.

Dakarun haɗin gwiwa da ke Kano sun dakile harin cikin gaggawa tare da yi wa ’yan ta’addan mummunar ɓarna, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa jihar Katsina, Sojojin sun bi sahunsu har zuwa ƙauyen Karaɗuwa da ke Ƙaramar Hukumar Matazu.

A wata sanarwa da Mai Taimaka wa Daraktan Hulɗa da Jama’a na Birgediya na 3, Major Babatunde Zubairu, ya fitar, ya ce bayanan leƙen asiri sun nuna cewa ’yan bindigar suna gudanar da jana’izar abokansu da aka kashe a yankin Ɗan Marke, a Ƙaramar Hukumar Matazu, lokacin da dakarun sama suka ga motsinsu.

Sanarwar ta ce an ci gaba da bibiyar su har sai da suka haɗu da baburansu bayan sun ƙetare wani busasshen kwarin rafi, inda jiragen yaƙin sama suka kai musu luguden wuta.

Rundunar ta bayyana cewa an hallaka akalla ’yan ta’adda 23, yayin da ake kyautata zaton wasu da dama sun samu raunuka kuma harin ya kuma lalata makamai da kayan aiki da dama na ’yan bindigar.

Kwamandan Birgediya na 3 ya yaba da jarumtaka da jajircewar dakarun sama da na ƙasa, yana mai cewa sun nuna bajinta na musamman a fagen yaƙi.

Rundunar Soja ta tabbatar wa al’ummar jihar Kano cewa yankin na ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali, tare da ci gaba da sintiri da sa ido a kai a kai.

Ta kuma gode wa jama’a bisa goyon bayan da suke bayarwa a yaƙi da ’yan ta’adda, tare da kiran su da su ci gaba da samar da bayanai cikin lokaci domin taimaka wa jami’an tsaro wajen dakile ayyukan ta’addanci.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba
Next Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari

Karin Labarai Masu Alaka

An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
Farmakin Da Aka Kai Makarantar Mata A Iran Yayi Ajalin Yara Da Dama Afrika
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
  • Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.