Sojoji sun kama ƙarin mutane 8 da ake zargi da hannu a harin bam na masallacin Borno
Sojojin rundunar Operation Hadin Kai sun kama ƙarin mutane takwas da ake zargi da hannun su a harin bam da wani mai tayar da kai ya kai a wani masallaci da ke Maiduguri, jihar Borno.
Wannan na zuwa ne kasa da kwana uku bayan sojoji sun kama wanda ake zargin shine ya shirya harin, mai suna Sheriff Umar, a babban birnin jihar.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa harin kunar bakin wake ya faru ne a ranar 24 ga Disamba na shekarar 2025, lokacin da wani mai tayar da bam ya tarwatsa na’urar fashewa (IED) a cikin wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla masu ibada biyar tare da jikkata wasu 35.
A cikin wata sanarwa, jami’in hulda da jama’a na rundunar Operation hadin kai, Sani Uba, ya bayyana cewa an kama waɗannan mutanen ne a wani samame da aka gudanar a unguwar Yan Lemu da ke karamar hukumar Mubi ta Kudu a Jihar Adamawa.
Ya ce, Binciken da aka yi a gidan da ake zargin ya haifar da gano maƙudan kuɗaɗe, wayoyin hannu, takardun shaidar tantancewa, katunan ATM, kayan ado da wasu kayan sirri na amfanin kai, waɗanda a halin yanzu haka ake gudanar binciken shaidu akan su.
Ya ƙara da cewa, wani da ake tsare da shi tuni ya tantance wasu daga cikin manyan masu hannu a lamarin a matsayin waɗanda suka kawo kayan da aka yi amfani da su wajen ƙera bam ɗin.
Ya ƙara da cewa, Sauran mutanen da ke zaune a gidan suma an samo alaƙarsu da wannan ƙungiya.


