Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kama Maharan Bom Din Maiduguri
Published: January 7, 2026 at 5:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sojoji sun kama ƙarin mutane 8 da ake zargi da hannu a harin bam na masallacin Borno

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai sun kama ƙarin mutane takwas da ake zargi da hannun su a harin bam da wani mai tayar da kai ya kai a wani masallaci da ke Maiduguri, jihar Borno.

Wannan na zuwa ne kasa da kwana uku bayan sojoji sun kama wanda ake zargin shine ya shirya harin, mai suna Sheriff Umar, a babban birnin jihar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa harin kunar bakin wake ya faru ne a ranar 24 ga Disamba na shekarar 2025, lokacin da wani mai tayar da bam ya tarwatsa na’urar fashewa (IED) a cikin wani masallaci da ke kasuwar Gamboru a Maiduguri, wanda ya yi sanadin mutuwar akalla masu ibada biyar tare da jikkata wasu 35.

A cikin wata sanarwa, jami’in hulda da jama’a na rundunar Operation hadin kai, Sani Uba, ya bayyana cewa an kama waɗannan mutanen ne a wani samame da aka gudanar a unguwar Yan Lemu da ke karamar hukumar Mubi ta Kudu a Jihar Adamawa.

Ya ce, Binciken da aka yi a gidan da ake zargin ya haifar da gano maƙudan kuɗaɗe, wayoyin hannu, takardun shaidar tantancewa, katunan ATM, kayan ado da wasu kayan sirri na amfanin kai, waɗanda a halin yanzu haka ake gudanar binciken shaidu akan su.

Ya ƙara da cewa, wani da ake tsare da shi tuni ya tantance wasu daga cikin manyan masu hannu a lamarin a matsayin waɗanda suka kawo kayan da aka yi amfani da su wajen ƙera bam ɗin.

Ya ƙara da cewa, Sauran mutanen da ke zaune a gidan suma an samo alaƙarsu da wannan ƙungiya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda
Next Post: Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa

Karin Labarai Masu Alaka

Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.