Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya
Published: January 10, 2026 at 3:06 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 11, 2026

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana aniyarta ta sake ƙarfafa dakarun tsaron ƙasar, domin tunkarar matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassa.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ne ya bayyana hakan a yayin taron addu’o’i na musamman da aka shirya domin dakarun tsaron ƙasa a Babban Masallacin Ƙasa da ke Abuja.

Shettima ya yaba da jajircewa da sadaukarwar da dakarun tsaron ƙasar ke yi, musamman waɗanda suka rasa rayukansu a bakin aiki wajen kare martaba da ikon ƙasar, da kuma rayuka da dukiyoyin al’umma.

Taron addu’o’in ya gudana ne a matsayin wani ɓangare na bukukuwan ranar tunawa da gudunmowar da dakarun tsaron Najeriya ke bai wa ƙasa.

Gwamnatin Tarayya ta ware ranar 15 ga watan Janairu na kowace shekara domin karrama dakarun tsaron ƙasar.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano
Next Post: NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.