Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland
Published: January 15, 2026 at 4:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani babban jami’in kasar denmark, yace har yanzu akwai abinda ya kira “babban sabani mai tushe a tsakaninsu da shugaba Donald Trump na Amurka a game da yankin Greenland, a bayan tattaunawar da suka yi a fadar White House da mataimakin shugaban Amurka JD Vance da sakataren harkokin waje Marco Rubio.

Amma kuma sassan biyu sun yarda zasu kafa wani kwamitin hadin guiwa domin tattauna hanyoyin warware sabanin da suke da shi a yayin da shugaba Trump ya ci gaba da nacewa a kan lallai sai dai Amurka ta karbi wannan yanki mai karamin ikon cin gashin kai daga hannun kawarta na kungiyar kawancen tsaron NATO, Denmark.

Trump ya yana kokarin nuna cewa ya kamata NATO ta taimaka ma Amurka wajen mallakar wannan tsibiri da ya fi kowanne girma a duniya, yana mai fadin cewa ba zai yarda da duk wani abinda zai gaza komawar yankin na Greenland hannun Amurka baki dayansa ba.

A halin da ake ciki, kasar Denmark ta bayyana shirye shiryen bunkasa yawan sojojinta a yankin tekun Arctic da arewacin tekun Atlantika a yayin da Trump yake wannan kokari nasa na mallakin Greenland.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula
Next Post: Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
  • Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.