Kasar Libya zata gurfanar da wani dan kungiyar ‘yan ta’adda da ake zargin sa da hannu a wani kabari da aka gano gawawwakin mutane 25 don tuhumar sa da laifin fataucin mutane, a cewar ofishin Antoni janar na Libya ranar Jumu’a.
A shafin sa na Facebook, ofishin ya ce an aike wanda ake tuhumar zuwa kotu amma hukumomi sun samu hujjoji cewa ‘yan ta’addan sun shirya hijira da fataucin mutane kan hanyar da ta saba wa doka a birnin al-Kufra dake kudu maso gabashin Libya, da kuma birnin Ajdabiya da ke yankin gabashin kasar kuma Ofishin Antoni janar din be fadi sunan kungiyar ba.
Libya de ta kasance hanya babba da ‘yan gudun hijira ke amfani da ita wajen gujewa yaki da talauci a Afirka da Gabas ta Tsakiya.
Ba’a samu cikakken bayanin yadda masu hijirar su 21 suka rasa rayukan su ba, da kuma lokacin da suka rasu da lokacin da aka gano gawawwakin na su ba.
Ranar Juma’a ofishin Antoni janar na Libya ya fitar da hotuna da ke nuna gawawwakin rufe cikin bakaken ledoji.


