Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025.
Published: January 19, 2026 at 6:51 AM | By: Bala Hassan

Senegal ta lashe gasar cin kofin kasashen nahiyar afirka Afcon na shekarar 2025.

A ranar Lahadi 18/01/2026 an fafata a wasan karshe na gasar cin kofin kwallon kafa ta kasashen Afirka wadda ya guda a Kasar Moroko.

Senegal ce ta lashe gasar akan masu masaukin baki kasar Moroko da ci 1-0 bayan da akwa kwashe mintoci 120, ana fafatawa.

Pape Gueye ne ya jifa kwallo daya tilo da ta ba Senegal nasara a cikin mintuna na 94, cikin karin lokaci na minti 15 din farko (Extra time).

A lokacin da ake cikin wasan Senegal ta fice daga filin wasa saboda rashin amincewa da bugun daga kai sai maitsaron raga da aka ba wa Moroko a ƙarshen mintuna 90 din farko bayan da da alkalin wasa ya duba na’ura mataimakawa alkalin wasa na VAR an kwashe tsawon minti 14 kafin daga bisani Senegal ta dawo, aka buga sai dai Ibrahim Diaz, ya zubar da fenaretin bayan da mai tsaron ragar Senegal Mendy ya cafke da hannunsa.

An bada manyan kyautuktuka guda uku Brahim Diaz dan wasan Moroko ya lashe kyautar wadda ya fi zura ƙwallo a gasar ta Afcon.

Sai mai tsaron ragar Moroko Yassine Bounou, shi ne mai tsaron raga mafi hazaka.

Dan wasan Senegal Sadio Mane shi ne ɗan wasa mafi kwazo a gasar afcon ta bana.

Shugaban hukumar wasan kwallon kafa ta Duniya Fifa Gianni Infantino ne ya miƙa kofin na Afcon wa Sadio Mane.

Kalidou Koulibaly ne kyaftin din Senegal sai dai bai buga wasan karshen ba saboda an dakatar da shi, amma ya zo wurin mika kofi sanye da kayan wasan Senegal.

Yayin da ‘yan wasan Senegal suke murnan lashe gasar sukuwa wasu da cikin yan wasan Moroko an hangosu suna ta sharban kuka ne bayan tashi a wasan.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027
Next Post: Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
Barcelona na hangen Enrique Ko Arteta Wasanni
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.