Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki
Published: January 20, 2026 at 8:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Togo ta kama tsohon shugaban kasar Burkina Faso, kuma ta tusa keyarsa zuwa kasar sa, bayan da jami’ai a Ouagadougou suka yi zargin yana kitsa juyin mulki, kamar yada wasu majiyoyi biyu suka fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar talata.

Paul Henri Damiba, ya hau mulki ne a shekara ta 2022 sakamakon juyin mulki da sojoji suka yiwa gwamnatin farar hular kasar, wacce tayi bakin jini saboda yadda ‘yan tawaye masu ikirarin Islama suke tada kayar baya.

Sai dai shi ma Damiba, da ya kasa shawo kan fitinar ‘yan bindigar, lamarin ya harzuka dakarun kasar dake yammacin Afirka, shi ma aka yi masa juyin mulki a cikin shekarar da ya hau mulki, mataki da ya kawo shugabancin Ibrahim Traore, wanda yake ci gaba da mulkin kasar.

A farkon wannan wata, Burkina Faso tace ta wargaza wan yunkurin kashe Troare, da take zargin Damiba da kullawa, wanda yake zaman gudun hijra a Lome babban birnin kasar Togo.

Wata majiya ta fuskar tsaro, da wata majiya kusa da fadar shugaban kasar Togo, sun gayawa Reuters a ranar talata cewa, an kama Damiba, ranar Asabar, kuma an maida shi Burkina Faso.

A dai ranar Talatan gwamnatin kasar Togo ta tabbatar da wannan labari, kuma cikin sanarwar da ta bayar wacce aka rubuta ranar Litinin, sannan aka raba, Damiba, yana fuskantar zargin almubazzaranci da dukiyar al’umma, arzurta kansa ba bisa ka’ida ba, rashawa da kuma halatta kudaden haram, amma sanarwa bata ambaci zargin juyin mulki ba.

Kamfanin dillancn labarai na Reuters, ya kasa magana da Damiba, kuma babu tabbas ko yana da lauya a Togo. Gwamnatin Burkina Faso, bata maida martani ba da aka nemi jin ta bakinta.

Afrika, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB
Next Post: Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
  • Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
  • An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.