Shugaban mulkin soja a Mali, ya kirkiro mukami daidai da minista, don kula da harkokin hakar ma’adinai a kasar, mataki da zata baiwa shugaban mulkin sojan damar kara sa ido kan harkoki da suka shafi wannan bangare, ya kuma nada wani dan kasar wadda a baya ma’aiakcin babban kamfanin hakar ma’adinai daga kasar Canada ya rike wannan mukami.
Takardun gwamnati sun nuna cewa mai rike wannan sabon mukami, yana da ikon sa ido ganin an aiwatar da manufofin gwamnati game da hakar ma’adinai, tabbatar da ana mutunta sharuddan, da sake nazarin rahotanni da masu hakar ma’adinai suke bayarwa, wadda a ada duka wannan yana karkashin ma’aikatar kula da harkokin ma’adinai ne.
Kamar yadda bayanai suka nuna, jami’in wanda kwararre ne ta kimiyyar albakatun kasa, a bara ne ya sauya sheka, daga zama wakilin kamfanin hakar ma’adinai na kasar Canada, zuwa bangaren gwamnati lokacin da gwamnatin take rikici kan iko da wurin haka’ar zinari mafi girma a kasar da kamfanin na Canada yake rike da shi.
Duk kokarin jin ta bakin jami’in Hillaire Bebian Diarra, wanda shine jam’in da shugaban Mali ya nada kan wannan sabon mukami ya ci tura.


