Amurka ta yi wa manyan ‘yan siyasar Iraq barazanar sawa kasar takunkumi, ciki har da arzikin da ake samu daga man fetur, idan aka bawa ‘yan tawaye da Iran ke marawa baya matsayi a gwamnatin da zata yi mulki a gaba, kamar yadda wata majiya ta shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters.
Wannan barazana na daga cikin irin matakan da Shugaba Donald Trump ke dauka wajen ganin ya raunana tasirin da ‘yan tawaye masu alaka da Iran suke da shi a kasar Iraq.
Wakilin jakadancin Amurka a Baghdad, Joshua Harris ne ya kai sakon barazanar, a wata tattaunawa da ya yi da jami’an Iraq, da kuma shugabannin Shi’a, a cewar Jami’an Iraq, ta kuma wani da ya yayi wa kamfanin dillacin labarai na Reuters bayani game da labarin.
Tun bayan da ya hau mulki shekara daya da ta wuce, Trump abubuwa na kokarin durkusar da gwamnatin Iran, ciki har da biyowa ta makwabciyar ta Iraq.


