Tsohuwar ministar albarkatun man fetur ta Nigeria Diezeni Allison Madueke ta karbi cin Hanci, ciki har da kayan sawa, da amfani da manyan gidaje mallakin ‘yan kasuwa masu bukatar kwangiloli masu tsoka daga masana’antar man fetur da na iskar gas, a cewar masu gabatar da kara, yayin gurfanar da ita gaban kotu ranar Talata.
Allison Madueke ta rike mukamin ministan albarkatun man fetur na kasa tsakanin shekarar 2010 zuwa 2015, karkashin mulkin Goodluck Jonathan, kuma ta rike mukamin shugaban kasashe masu arzikin man fetur wato OPEC, na kankanin lokaci. Ta kasance mace ta farko da ta rike duk wadannan mukamai.
Allison Madueke me shekaru 65 a duniya ta kasance daya daga cikin fitattun jami’an da suka rike mukami a fannin makamashi da ke fuskantar tuhuma a kotu kan aikata laifin almundahana, bayan an tuhume ta a shekarar 2023 da laifuka biyar na karban cin hanci, da kuma yin makarkashiyar bada cin hanci, abin da ta Musanya.
Mai gabatar da kara Alexandra Healy ta fada a wata kotu da ke birnin Landan, cewa Allison Madueke na zaman daula ne a Landan inda ta ke yawan zama, daga abin da take samu daga mutane masu bukatar kwangila daga kamfanonin Nigeria.
Healy ta ce an bawa Allison Madueke damar zama a gidaje masu alfarma, da kuma amfani da kayan alatu masu tsada, daga mutanen da suka yarda cewa zata yi amfani da mukamin ta don samar musu abin da suke bukata.
Ta kara da cewa, babu wata hujja da ta nuna cewa Allison Madueke ta bada kwangila ga wadanda basu cancanta ba, amma ba daidai bane ta karbi kyaututtuka daga wadanda ke kawsuwanci da kamfanonin gwamnati.
Allison Madueke ta zauna a akwatin tuhuma a kotu tare da wata mai zartarwa a kamfanin man fetur, Olatimbo Ayinde, me shekaru 54, wadda ake tuhuma da laifi daya na acin hanci, da yake alaka da Allison Maduek, da kuma wani laifin da ban na tuhumar bawa jami’in gwamnatin wata kasa cin hanci.
Yaya ga Allison Madueke, Doye Agama, me shekaru 69, shi ma ana tuhumar sa da kulle-kullen bada cin hanci da ke da alaka da cocin sa, kuma yana sauraron karar ne da hanyar video saboda dalilin rashin lafiya.
Ayinde da Agama ma sun musanta zargin da ake yi a kan su.
Ana zargin Allison Madueke da Karbar kayayyakin kudade daga mutane da ke da alaka da masana’antun man fetur na Nigeria, da suka hada da amfani da mota da direba da jirgin saman yawo.
An kuma zarge ta da sa wani dan kasuwa a Nigeria, Benedict Peters da biyawa dan ta kudin makaranta, wanda akwai sunan sa a tuhumar, amm ba zai fuskanci shari’a ba.


