A wani hari mafi tsanani cikin makon nin nan, da Isra’ila ta kai a Gaza a ranar Asabar, ya kashe mutane 27 ciki harda yara uku a farmakin data auna kan ofishin ‘Yan sanda, da gidaje da kuma akan tantuna, kamar yadda jami’n kiwon lafiya a yankin Falasdinu suka fada.
Sojojin Isra’ila suka ce sun auna hare haren ne akan wasu kwamandoji da wasu wurare dake ƙarƙashin mayakan sakai na Hamas da kawarta Islamic Jihad, a zaman martani na zargin keta yarjejeniyar tsagaita wuta, da Amurka ta shiga tsakani aka kulla a watan oktoban bara, bayan shekara biyu na yaki a Gaza.
Hamas wacce yanzu take da iko kasa da rabin Gaza, tace Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita wutar. Sai dai bata fadi ko harin da Isra’ilan ta kai ya afkawa wakilanta ko muhallai da take iko da su.
Isra’ila ta kai harin ne kwana daya gabannin bude kan iyakar Gaza da Masar, karkashin shirin shugaban Amurka Donald Trump na kawo karshen yakin, wadda kusan ya rusa komi a Gaza.
A halinda ake ciki kuma, mutane 4 sun mutu, sakamakon fashewar iskar Gas a wasu gidaje a wurin da ake kira Ahvaz a Iran.


