A Kasar Pakistan dubban mutane ne suka hallara ranar Asabar, domin jana’aizar mutane 33 wadanda suka halaka sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a wani masallacin ‘yan shi’a lokacin jumma’a, an tsaurara matakan tsaro a birnin, kuma hukumomin kasar suka ce sun kama mutane hudu wadanda suka hakikance sun taimakawa wanda ya kai harin.
A harin na ranar Jumma’a, mutumin ya fara da harba bindiga a masallacin da ake kira khadijatul kubra da yake bayan garin babban birnin kasar, daga bisani ya tada bam wanda ya halaka mutane 32, tare da maharin, ya kuma raunata mutane sama da 170.
Ministan harkokin cikin gidan kasar Moshin Naqvi, ya fadawa wani taron manema labarai cewa mutane hudu ciki harda jagoran kitsa kai harin suna hanu, bayan wani matakin da kasar ta dauka a Peshwar da kuma Nowshera.
A lokacin matakin, ministan yace wani jami’in yaki da ta’addanci daya ya mutu,wasu uku kuma suka jikkata.
Kungiyar ISIS ta duki alhakin kai wannan mumunar hari, hari mafi muni da aka jima ba’a ga irinsa ba a Islamabad babban birnn kasar.


