Ministan harkokin wajen Habasha ya zargi makwabciyarta Eritriya da laifin cin zarafin soji da kuma goyon bayan kungiyoyin dake dauke da makamai a cikin kasar Habasha, kamar yadda wata wasika da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani, kuma ma’aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar da hakan.
Kasashen biyu makota dake nuna kiyayya ga juna, sun dade suna yaki da juna tsakanin 1998 zuwa 2000, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a shekarar 2018 kuma sun kasance kawaye a yakin shekaru biyu na Habasha da mahukuntan yankin a arewacin yankin Tigray.
Sai dai Eritrea ba ta cikin yarjejeniyar 2022 da ta kawo karshen rikicin yankin na Tigray, kuma dangantaka tsakanin kasashen biyu ta shiga tsaka mai wuya tun lokacin.
Rikicin baya-bayan nan tsakanin dakarun Tigrai da sojojin Habasha ya haifar da fargabar sake komawa yaki.
Wani mai magana da yawun gwamnatin Eritrea ya ce jami’ai na duba ko an kai wa ma’aikatar harkokin wajen kasar wasikar.


