A wani rahoto da kamfanin dillancin labarai Reuters ya bayar, yace Ethiopia ko Habasha ta bude wani sansani cikin sirri inda ake horas da dubban dakarun wucin gadi na RSF a sudan, mataki da yake kara nuni da yadda yakin na Sudan ya kara janyo tsoma bakin manyan kasashe daga Afirka da kuma gabas ta tsakiya.
Sansanin shine kwakkwaran shaidar cewa Ethiopia tana da hanu a yakin basasar da akeyi a Sudan, mataki mai hadarin gaske saboda zai ci gaba da samarwa kungiyar ‘yan tawayen RSF sabbin dakaru a yayinda yaki yake kara tsanani a kudancin Sudan.
Majiyoyi daban daban har takwas, ciki harda manyan jami’an gwamnatin Habasha suka ce hadaddiyar daular larabawa ce ta dauki nauyin gina sansanin, kuma ta samarda sojoji da za su horasda dakarun na RSF da kuma sauran bukatu a sansanin, kamar yadda rubutattun bayanai daga jami’an Habasha da kuma ta kafofin difilomasiyya da kamfanin dilancin labarai na Reuters ya gani.
Reuters ba zai tantance kai tsaye rawar da hadaddiyar daular larabawa take takawa a aikin gina sansanin. Da ka tuntube ta kan wannan lamari, ma’aikatar harkokin wajen daular tace bata da hanu ta ko wani fuska a yakin basasar da take ci a Sudan ahalin yanzu.


