Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON
Published: February 11, 2026 at 4:37 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya nada Amb Isma’il Abba Yusuf a matsayin sabon shugaban hukumar kula da aikin hajji ta Najeriya NAHCON

Shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu ya nada Ambasada Ismail Abba Yusuf a matsayin sabon Shugaba hukumar kula da aikin hajji ta kasa, NAHCON. Nada shi na bukatar amincewar Majalisar Dattawa kamar yadda dokar NAHCON ta 2006 ta tanada.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara kan Yada Labarai, Mr Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Bola Tinubu ya aika wasika ga Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, yana neman majalisar ta tabbatar da nadin cikin gaggawa. Ambasada Ismail Abba Yusuf zai maye gurbin Farfesa Abdullahi Usman wanda ya yi murabus a wannan mako bayan shafe kusan watanni 14 a mukamin.

Sanarwar ta bayyana cewa Ambasada Ismail Abba Yusuf gogaggen jami’in diflomasiyya ne, wanda ya taba zama jakadan Nijeriya a kasar Türkiye daga 2021 zuwa 2024. Ana sa ran nadin nasa zai taimaka wajen ci gaba da tafiyar da harkokin aikin Hajji da ayyukan NAHCON.

Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar
Next Post: Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi

Karin Labarai Masu Alaka

An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.