A kalla mutane 50 ne suka rasa rayukansu sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai wani kauye a jihar Zamfara, tare da sace mata da yara da yawa, a cewar wani dan majalisa da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Jumu’a.
Hamisu A Faru, dan majalisa mai wakiltar Bukkuyum ta kudu ya ce, ‘yan ta’addan sun far ma kauyen Tungan Dutse wajen karfe biyar na yamma ranar Alhamis, suka ci gaba da tafka barna har zuwa 3:30 na wayewar safiyar Jumu’a, inda suka kokkona gidaje, suka kuma rika harbin mutanen da ke guduwa don tsira da ran su.
Ya ce har yanzu ba’a san adadin mutanen da aka sace ba.
Wani mazaunin wurin Abdullahi Sani, ya ce kwana daya kafin faruwar abun mazauna kauyen sun tuntubi jami’an tsaro lokacin da suka ga babura fiye da 150 dauke da mutane, amma babu abin da aka yi a kai.


