Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma’a ta ce, taimakon abinci da abinci mai gina jiki na ceton rai a Somaliya zai iya tsayawa nan da watan Afrilu matukar ba a samar da wani sabon tallafi ba, lamarin da ke jefa miliyoyin mutane cikin hadarin tabarbarewar yunwa.
Kimanin mutane miliyan 4.4 ne ke fuskantar matsalar karancin abinci, inda kusan miliyan daya daga cikinsu ke fama da matsananciyar yunwa, saboda illar rashin damina da tashe-tashen hankula da raguwar kudaden agaji, in ji WFP.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ross Smith, darektan shirye-shiryen bayar da agajin gaggawa na WFP, ya ce “Al’amarin yana kara tabarbarewa cikin wani yanayi mai ban tsoro.”
“Iyalai sun yi hasarar komai, kuma an riga an shiga cikin tsaka mai wuya. Idan ba tare da tallafin abinci na gaggawa ba, yanayi zai kara tsananta cikin sauri,” in ji Smith.


