Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya
Published: February 23, 2026 at 4:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar samar da abinci ta Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma’a ta ce, taimakon abinci da abinci mai gina jiki na ceton rai a Somaliya zai iya tsayawa nan da watan Afrilu matukar ba a samar da wani sabon tallafi ba, lamarin da ke jefa miliyoyin mutane cikin hadarin tabarbarewar yunwa.

Kimanin mutane miliyan 4.4 ne ke fuskantar matsalar karancin abinci, inda kusan miliyan daya daga cikinsu ke fama da matsananciyar yunwa, saboda illar rashin damina da tashe-tashen hankula da raguwar kudaden agaji, in ji WFP.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ross Smith, darektan shirye-shiryen bayar da agajin gaggawa na WFP, ya ce “Al’amarin yana kara tabarbarewa cikin wani yanayi mai ban tsoro.”

“Iyalai sun yi hasarar komai, kuma an riga an shiga cikin tsaka mai wuya. Idan ba tare da tallafin abinci na gaggawa ba, yanayi zai kara tsananta cikin sauri,” in ji Smith.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya
Next Post: Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Birai Afrika
Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
Sojojin Amurka Sunfara Isowa Gabas Ta Tsakiya Amurka
Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.