Dakarun sa kai a Sudan sun kai farmaki wani gari a lardin Darfur, inda wani basarake ke da karfin iko, har suka yi sanadiyyar rayukan mutane a kalla 28, a cewar Wasu kungiyar likitoci a ranar Talata.
Dakarun sa kai na RSF sun tasamma garin Misteriha da ke arewacin lardin Dafur ranar litinin. Garin kuma yana karkashin ikon Musa Hilal, wanda ya fito daga kabilar larabawa ta Rizeigat, inda yawanci ‘yan kungiyar ta RSF suka fito daga ciki.
A kalla mutane 39, cikin su har da mata goma suka jikkata. Ba’a de san musabbabin da ya sa dakarun na RSF suka kaiwa garin hari ba.
An fara yaki a Sudan tun shekarar 2023 bayan da dangantaka tsakanin sojojin Sudan da dakarun sa kai na RSF tayi tsamin da har ta kai ga barkewar yaki da ya fara daga Khartoum, babban birnin kasar, sannan ya barbazu ko ina cikin kasar.


