A jamhuriyar demokuradiyyar Kwango, an gano manyan kaburbura 2 dauke da gawarwakin mutane 172 a birnin Uvira dake gabashin kasar bayan da ‘yan tawayen kunigyar AFC/M23 suka janye daga birnin, kamar yadda wani babban jami’in gwamnatin kasar ya fada.
‘Yan tawayen sun kama birnin Uvira na wani dan gajeren lokaci, wadda wurin yada zango ne a gabar tabkin Tanganyika kusa da kan iyakar kasar da Burundi a cikin watan Disemba. Suka kuma fara janyewa bayan mako daya sakamakon matsin lamba daga Amurka, mataki da ya kai ga sojojin Kwango suka sake shiga birnin a cikin watan jiya.


