Fadar Shugaban Ƙasar Najeriya ta ƙaryata jita-jitar da ke yawo cewa an kama wani ma’aikacin ɗakin girki na Fadar Aso Rock bisa zargin yunƙurin sa guba ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.
Mai bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga, ne ya fitar da sanarwar da ke musanta labarin, inda ya bayyana cewa rahoton ba gaskiya ba ne.
A cewarsa, babu wani ma’aikacin ɗakin girki na Fadar Aso Rock da aka kama, haka kuma babu wanda ya yi yunƙurin sa guba ga Bola Ahmed Tinubu.
“Babu wani ma’aikacin ɗakin girki na Aso Rock da aka kama. Babu kuma wani ma’aikacin da ya yi yunƙurin sa guba ga Shugaba Tinubu. A yi watsi da wannan labarin ƙarya da ake yaɗawa ta wani bidiyo,” in ji sanarwar.
Fadar ta buƙaci al’umma da su yi taka-tsantsan da labaran da ba a tabbatar da sahihancinsu ba, tare da yin watsi da jita-jitar da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta.


