Shugaban kasar Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya zabi Taiwo Oyedele a matsayin karamin ministan kudi bayan da ya jagoranci gyara bangaren haraji na kasa, a cewar fadar shugaban kasar ranar Talata.
Oyedele, mai shekaru 50 da haihuwa, wanda da shine shugaban kwamitin shugaban kasa kan kasafin kudi da sabbin sauye-sauyen haraji, ya maye gurbin oris Uzoka-Anite, wadda za’a mayar ita ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren kasa.
Tinubu ya aikewa da majalisar dattijai sunan Oyedele don tabbatar da shi, a cewar mai magana da yawun fadar shugaban kasa Bayo Onanuga.


