Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato
Published: March 6, 2026 at 1:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani sako cikin murya da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani ya tada hankalin mazauna garin Jos da kewaye.
Mai maganar, a cikin dakika talatin da takwas an jiyo shi yana shaida wa wani cewa kada ya fito daga gidanshi saboda za’a yi zanga-zanga a Jos.
Muryar da ta karade shafukan sada zumunta ta sanya fargaba a zukatan mutane da waswasin hana ‘ya’yansu zuwa makaranta da fita kasuwanci.
Kan haka ne kwamishinan ‘yan sanda na jihar Filato, Bassey Ewah ya kira taron gaggawa da matasan kungiyar Islamic Movement of Nigeria wato kungiyar Shi’a don jin karin bayani kan ko suna shirin yin tattaki ne, ganin yadda ya gudana a wassu jihohin Najeriya, biyo bayan yakin dake aukuwa tsakanin kasar Amurka da Isra’ila da Iran.
Adam Khalid Muhammad shine wakilin dalibai na kungiyar ‘yan’uwa Musulmi a Najeriya, reshen jihar Filato, dake karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim El-zakzaki yace sun shaida wa komishinan ‘yan sandan cewa basu san inda maganar zanga-zanga ta bullo ba.
Shima jagorar kungiyar a Jihar Filato, Sheikh Muhammad Auwal Abubakar yace kungiyarsu tana da tsari na mutunta ‘yancin kowa, don haka basu da niyyar tozarci ko kuntata wa kowa.
Rundunar ‘yan sandan ta jihar Filato dai ta kara tsaurara matakan tsaro a cikin garin Jos, musamman a unguwannin da take kira Flash Points, wato wuraren da ke da barazanar barkewar rikici, ciki har da kasuwanni.
Wakiyar Amurka Ke Magana a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/RADE-RADIN-ZANGA-ZANGA-A-JOS.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya
Next Post: Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Yace Sojojin Amurka Dana Iran Sunyi Taho Mugama Amurka
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya Najeriya
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Jihohin Arewaci Sun Kafa Asusun Yaki Da Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.