A Jamhuriyar Congo an kada kuri’a a zaben shugaban kasa ranar Lahadi, wanda ake sa ran zai tsawaita wa’adin mulkin shugaba Denis Sassou Nguesso, daya daga cikin shugabannin Afirka da suka fi dadewa akan karagar mulki, duk kuwa da cewar mutane basu fito da yawaba don kada kuri’unsu.
Sassou na fuskantar wani kalubale daga abokan hamayya, tare da saka wasu fitattun jagororin adawa na kasar a gidan yari, wasu kuma suna gudun hijira. Jam’iyyun adawa da dama sun kauracewa zaben, suna masu cewa tsarin ba shi da inganci.
Fiye da ‘yan Kwango miliyan 3.2 ne aka yi wa rajista don kada kuri’a, ko da yake masu sharhi da kungiyoyin fararen hula sun yi hasashen cewa za a kada kuri’u kusan kashi 68 cikin dari da aka samu a shekarar 2021, lokacin da Sassou ya lashe wa’adinsa na shekaru biyar da suka gabata da kashi 88.4% na kuri’un.
Wani ya shaidawa Reuters cewa, an samu gajerun layuyuka na masu kada kuri’u a mafi akasarin rumfunan zabe a Brazzaville babban birnin kasar.
Bayan da ya kada kuri’arsa a Brazzaville, Sassou ya shaidawa manema labarai cewa yana fatan kwarin gwiwar da ya ce ya gani a fagen yakin neman zabe za ta fito fili a sakamakon karshe.
“Muna fatan abin da na ji a duk lokacin yakin neman zabe zai tabbata a yau,” in ji shi.


