Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Bauchi ta yi Allah wadai da mummunan hari da wasu jami’an ‘yan sanda suka kai wa ma’aikatan gidan rediyon Albarka a Bununu, Tabawa Balewa LG, Jihar Bauchi a lokacin bikin Sallah.
“Wannan mummunan aiki na ta’addanci babban take hakkin dan adam ne, kuma ya zamo karan tsaye ga ‘yancin manema labarai, da kuma nuna rashin bin doka da oda daga jami’an da ake sa ran za su kare lafiya da dukiyoyin al’uma, ba cutar da ‘yan ƙasa ba.
Abin damuwa ne musamman ganin irin wannan rashin da’a yana faruwa a daidai lokacin da NUJ ke ƙara himma wajen fafutukar neman ƙwarewa da riƙon amana tsakanin hukumomin tsaro. ” inji ta.
Takardar dauke da sa hanun Sakataren ta na Jiha Isah Garba Gadau, an wallafa a ranar Litinin 23/03/2026
ta buƙaci Kwamishinan ‘Yan Sanda, na Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya gaggauta bincika lamarin tare da hukunta duk jami’in da aka sa me shi na da hannu a wannan mummunan aiki.
Bugu da ƙari, Ƙungiyar ta ce dole ne, ba tare da ɓata lokaci ba, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Bauchi ta ɗauki alhakin biyan duk wani kuɗaɗen magani da wanda abin ya shafa ya kashe.
Idan kuma ba a cika waɗannan buƙatun ba, Ƙungiyar za ta kira taron gaggawa don yanke shawara kan mataki na gaba.
Ta kuma ƙara kira ga dukkan kafafen yaɗa labarai a jihar da su kasance cikin shiri kuma su jira ƙarin umarni domin Ƙungiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba har sai an yi adalci kuma an tabbatar da tsaron ‘yan jarida da kare musu mutuncinsu.
Ƙungiyar NUJ ba za ta lamunci cin zarafi, ko cin mutumcin ga ‘yan jarida a kowane hali ba.
In za’a iya tunawa a ranar lahadi 22 ga watan Maris 2026, kafan sadarwar zamani da kuma manyan gidajen jarida su ka wallafa hoton wani dan Jarida mai suna Muhammad Adamu ma’aikaci a gidan Rediyo Albarka da ke jihar Bauchi Arewa maso gabas a Najeriya cikin jini bayan da suka samu sa in sa tsakaninsa da Jami’in Dan Sanda mai kula da Division na Bununu da ke Karamar hukumar Tafawa Balewa Bauchi.
A cewar dan Jaridar ya je aiki ne dan dauko rahoton bukukuwar Sallah da ake yi a wannan gari ta Bununu, yayin da yazu shiga wajan sai DPOn ‘yan sanda na Bununu SP Jamilu Kabir da yaransa suka lakkada masa dukan kawo wuka har suka masa rauni a kansa ba tare da karya wata doka ba.
A bangaren ta rundunan ‘Yan Sanda na Jihar ta bakin Jami’in hulda da jama’anta SP Nafi’u Habib, ya ce sun samu labarin afkuwar lamarin suna kan bincike domin bin kadin duk mai gaskiya ta re da daukan matakin da ya dace a hukumance.


