Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, na gaggauta kokarin amincewa da kasafin kudin ƙasa domin kauce wa zabukan wuri-wuri da ake ganin zai iya sha kaye a cikinsu, yayin da yakin da ake yi da Iran bai kawo wani gagarumin sauyi a yadda ake kallonsa a kuri’un jin ra’ayin jama’a ba.
A kwanakin farko na yakin, bangaren Netanyahu ya ga wata dama ga kawancen jam’iyyunsa na dama su amfana da harin farko da ya kashe Ayatollah Ali Khamenei, ta hanyar gudanar da zabuka kafin lokacin da ake sa ran yi a watan Oktoba, kamar yadda wata majiya mai masaniya kan dabarun siyasarsa ta bayyana.
Daya daga cikin hanyoyin tilasta gudanar da zabukan gaggawa ita ce a bar majalisar dokoki ta kasa amincewa da kasafin kudin kafin ranar 31 ga Maris, wanda a karkashin dokar Isra’ila zai jawo gudanar da zabe cikin kwanaki 90. Yayin da hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra’ila suka kashe manyan jami’an Iran da dama, wasu na kusa da Netanyahu sun fito fili suna hasashen yiwuwar gudanar da zabe a watan Yuni.
Sai dai kusan makonni hudu da fara yakin, wanda har yanzu bai cimma daya daga cikin manyan manufofinsa na kifar da gwamnatin malaman addini ta Iran ba, firaministan Isra’ila mafi dadewa a mulki na kokarin kauce wa zabukan wuri-wuri, kamar yadda mambobi uku na gwamnatinsa suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.


