Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Anyi Jana’izar Mahaifiyar Nasiru El Rufai A Abuja
Published: March 29, 2026 at 2:04 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An gudanar da sallar jana’izar Hajiya Umma El-Rufai, mahaifiyar tsohon gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai, a National Mosque Abuja da ke birnin Abuja a Najeriya.

Jana’izar ta samu halartar manyan ‘yan Najeriya daga sassa daban-daban na rayuwa. Daga cikin waɗanda suka halarta akwai attajirin ɗan kasuwa Aliko Dangote, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu, da kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar.

Sauran sun haɗa da gwamnan Jihar Kaduna Uba Sani, gwamnan Jihar Borno Babagana Zulum, gwamnan Jihar Neja Mohammed Bago, da tsohon gwamnan Jihar Zamfara Abdulazeez Yari.

Haka kuma, jana’izar ta haɗa da halartar gwamnoni, sanatoci, sarakunan gargajiya, ‘yan kasuwa da sauran manyan shugabanni daga faɗin ƙasar.

An gudanar da jana’izar cikin yanayi na nutsuwa da jimami, inda aka yi addu’o’i domin Allah Ya jikanta da rahama, Ya kuma gafarta mata kurakuranta.

Afrika, Labarai, Najeriya, Rumbun Hotuna

Post navigation

Previous Post: Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP
Next Post: Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund

Karin Labarai Masu Alaka

Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
  • ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027 Shirye-Shirye
  • Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
  • Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.