Dubbannan sojojin Amurka masu dirga daga jiragen sama sun fara isowa Gabas ta Tsakiya, a cewar wasu jami’an Amurka biyu da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar Litinin, yayin da shugaba Donald Trump ke duba mataki na gaba da zai dauka a yakin da ake tafkawa da Iran.
Sojojin masu dirgowa daga jiragen sama da suka fito daga sansanin soji na Fort Bragg a jihar North Carolina, sun biyo bayan karin dubbannan matukan jirgin ruwa, sojin ruwa da kuma Dakaru na musamman da aka aike yankin. A karshen makon nan sojin ruwa kusan 2,500 ne suka isa Gabas ta Tsakiya.
Jami’an da suka nemi a sakaya sunayen su, basu fadi ainihin inda za’a tura sojojin ba. Daya daga cikin jami’an yace, ba’a yanke shawarar tura dakarun Iran ba tukun, amma zasu ci gaba da taruwa don aiki nan gaba a yankin.


