Gwamnatin jihar Filato ta ayyana dokar hana fita na kwanaki biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa.
Matakin ya biyo bayan wani harin kan-mai-uwa-da-wabi da ‘yan bindiga suka kai a Unguwar Rukuba dake cikin birnin Jos.
Harin da ‘yan bindigar suka kawo da misalin karfe takwas na daren Lahadi, bayanai daga shaidun gani da ido na nuni da cewa, ‘yan bindigar sun zo ne a kan babura da mota kirar sharon, wanda yayi kama da na jami’an dake yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi da fuskokinsu a rufe, suka bude wuta a wata mahada da ta kasance kamar kasuwa, ake hada-hada dare da rana.
A sanarwa da gwamnatin jihar Filato ta fitar da sanya hannun komishinan yada labarai da sadarwa na jihar, Madam Joyce Ramnap, matakin sanya dokar hana zirga-zirgar ya zama dole, don samadda damar shapke wadanda suka yi barnar don hukunta su.
Matakin shugaban karamar hukumar Jos ta Arewa, Muhammad Kabiru Garkuwa, yace an dade ba’a ga irin wannan mummunan lamari a cikin garin Jos ba, don haka hukumomi na yin duk mai yiwuwa wajen hana maida hannun agogo baya a lamarin tsaro.
Duk da shike hukumomi basu bada adadin wadanda suka rasa rayukansu a harin ba, wata mace da bata amince in bayyana ta ba, ta shaida min cewa ta ga gawarwaki talatin da uku.
Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya kai ziyarar jaje a Unguwar Rukuba, inda ya ba matasa hakurin kada su dauki doka a hannunsu, don kaucewa kashe wadanda basu ji ba basu gani ba.
Daga Jos Ga Rahoton Zainab Babaji


