Wani mutum dauke da adda ya hallaka yara hudu a wata makarantar nursery ta yara a Kamafala, babban birnin kasar Uganda a jiya Alhamis.
Mutumin ya samu shiga makarantar ne ta hanyar yin basaja a matsayin daya daga cikin iyayen yaran, a cewar wata jarida mai suna Daily Monitor. Da farko ya shiga ofishin shugaban makarantar, inda suka sha artabu, sannan ya fito ya kulle gate din makarantar ya far ma yaran.
Daga baya ‘yan sanda sun yi nasarar cafke mutumin. Har yanzu ba’a san dalilin da ya sa ya aikata wannan ta’asa ba. Hare-hare irin wannan bai cika faruwa a Uganda ba, kasar dake dauke da mutane kusan mutane miliyan uku.


