Babban bankin duniya World Bank ya rage hasashensa na bunƙasar tattalin arziki ga yankin Afirka da ke kudu da hamadar Sahara a shekarar 2026, a wani rahoto da ya fitar a jiya Laraba, yana mai cewa tasirin yaƙin Iran na hana farfaɗowar tattalin arzikin yankin.
Bankin yanzu na sa ran bunƙasar kashi 4.1% a 2026, wanda bai canza ba daga 2025, amma ya ragu daga hasashen kashi 4.4% da ya bayar a watan Oktoba. Bankin ya ce an rage waɗannan alkaluma ne tun bayan barkewar yaƙin Gabas ta Tsakiya a ƙarshen watan Fabrairu, wanda ya haifar da tashin farashin man fetur da takin zamani, tare da barazana ga zuba jari, yayin da nauyin basussuka masu yawa ke ci gaba da janyo koma baya ga bunƙasar tattalin arziki.
Wannan gargadi na zuwa ne a daidai lokacin da Washington da Tehran suka amince da tsagaita wuta na makonni biyu, duk da cewa U.S. Energy Information Administration ta yi gargadi a ranar Talata cewa farashin man fetur na iya ci gaba da tashi na tsawon watanni, ko da bayan sake buɗe mashigar Hormuz, wadda kusan kashi ɗaya cikin biyar na jigilar man duniya ke bi ta cikinta.
Babban masanin tattalin arziki na Afirka a Bankin Duniya, Andrew Dabalen, ya ce wannan ragin hasashe na nuna cewa yanayin tattalin arzikin duniya ya fi tsauri fiye da yadda masu tsara manufofi suka yi tsammani a ƙarshen shekarar da ta gabata.


