Shugaban Amurka Donald Trump ya ce a jiya Lahadi rundunar ruwan Amurka za ta fara kakabawa mashigar ruwa ta Hormuz takunkumi, lamarin da ke ƙara tsananta rikicin bayan tattaunawa mai tsawo da Iran ta kasa haifar da yarjejeniya don kawo ƙarshen yaƙin, tare da jefa yarjejeniyar tsagaita wuta ta makonni biyu cikin haɗari.
Rundunar Tsakiyar Sojojin Amurka (U.S. Central Command) ta bayyana cewa dakarun Amurka za su fara aiwatar da wannan takunkumi kan duk zirga-zirgar jiragen ruwa da ke shiga da fita daga tashoshin jiragen ruwa na Iran da misalin ƙarfe 10 na safe agogon Gabashin Amurka (1400 GMT) a yau Litinin.
Sanarwar rundunar da aka wallafa a shafin X ta ce za a aiwatar da wannan takunkumi “ba tare da nuna bambanci ba kan jiragen ruwa na kowace ƙasa da ke shiga ko fita daga tashoshin jiragen ruwa da yankunan gabar tekun Iran, ciki har da dukkan tashoshin Iran da ke Tekun Arabian Gulf da kuma Tekun Oman.”


