Dan hamayya daya a zaben shugabn kasar Benin, Paul Hunkpe ya amince ya sha kaye inda ministan kudi Romuald Wadagni ya saami nasara, kamar yadda tashar talabijn ta kasar ta bada sanarwa a jiya Litinin.
Dan shekaru 49 da haifuwa, tsohon babban ma’aikacin kamfanin Deloitte, Wadagni shine mutuminda shugaba mai barin gado ya zaba, kuma ya sami goyon bayan hadakar jam’iyu da suke mulkin kasar, a zaben da aka yi ranar Lahadi, wadda aka gudanar bayan wani yunkurin juyin mulki da aka so a yi a kasar watanni hudu da suka wuce.


