
ADC Ta Kaucewa Matakin INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Da Ya Tabbatar Da Jagorancin David Mark
Jam’iyyar adawa ta ADC ta gudanar da babban taro na kasa ta hanyar kin amincewa da matakin hukumar zabe na gargadin kar ta yi hakan.
Taron dai ya tabbatar da jagorancin Sanata David Mark wanda hukumar zabe ta cire sunansa da mai hamayya da shi a matsayin shugabanni bisa fassarar hukuncin kotu.
“A lokacin da APC ta hau mulki Najeriya na mataki na 8 na a ta’ddanci a duniya. Idan su ka kara wasu shekarun 4 Najeriya za ta dawo ta daya” Inji daya daga manyan ‘yan adawan na ADC Peter Obi wanda ke lissafa yadda gwamnatin Tinubu ta samu kasa da kuma yanda lamura su ke a yanzu.
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku ya yi dirar mikiya ne kan shugaban hukumar zabe Joash Amupitan da nuna ba zai sha su a masilla ba da matakan da ya ke dauka na takura adawa.
Adamu Hassan Bunun Kashere na daga mahalarta taron daga Arewa maso gabar, ya ce ba ya raba daya biyu ga tasirin da ADC za ta yi a babban zaben 2027.
Shi ma mukarrabin Peter Obi, Malam Ibrahim Hussaini Abdulkarim na kore tunanin za a samu Baraka a jam’iyyar wajen zaben fidda gwani a tsakanin manyan yan takara da su ka yi dafifi a jam’iyyar.
Taron dai ya gudana da amfani da na’urorin samar da wuta na janareta don tsinke wuta da mai dandalin taron ya yi bisa zargin an umurce shi ne ya yi hakan ko a soke lasisinsa na hurumin gudanar da fagen taruka wato EVENT CENTER na RAINBOW da ke anguwar Garki.
Kazalika taron ya kori shugaban bangare na jam’iyyar Nafiu Bala da wasu ‘yan jam’iyya da jagorancin Mark ya zarga da cin amana.

