Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
Published: April 17, 2026 at 12:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32.

Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Yadda Aka Rarraba Kasafin Kuɗin 2026

A cikin wannan gagarumin kasafi na naira triliyan 68.32, an ware Naira triliyan 4.799 Domin ayyukan da doka ta tanada (Statutory Transfers), sai Naira triliyan 15.8 Domin biyan basussukan da ake bin ƙasa. Naira triliyan 15.4 Domin kuɗaɗen gudanarwa (Recurrent Expenditure), sai Naira triliyan 32.2 Domin ayyukan raya ƙasa (Capital Expenditure).

Wannan kasafi ya nuna cewa kusan kashi 50 cikin ɗari na kuɗaɗen za su tafi ne ga ayyukan raya ƙasa, wanda hakan ke nuna ƙudurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tattalin arziki, tsaro, da gina ababen more rayuwa ga ‘yan Najeriya.

Tsawaita Lokacin Kasafin 2025

Baya ga sabon kasafin, Shugaba Tinubu ya amince da gyaran dokar kasafin 2025 domin ba da damar ci gaba da amfani da kuɗaɗen ayyukan raya ƙasa har zuwa ƙarshen watan Yunin 2026.

Manufar wannan mataki ita ce tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) sun kammala manyan ayyukan da suke hannunsu ba tare da cikas ba, musamman waɗanda suka riga suka yi nisa.

Umarni Zuwa Ga Ma’aikatu

Shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen cikin gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowace kwabo ta yi amfanin da aka nufa don amfanin talaka.

Haka kuma, ya jinjina wa shugabanni da mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa bisa jajircewa da kishin ƙasa da suka nuna wajen hanzarta duba tare da amincewa da wannan kasafi.

A ƙarshe, Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a ɓangaren tattalin arziki don samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
Next Post: Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
Bincike Yanuna Kasashen Afirka Suna Cikin Mafiya Cin Bashi A Duniya Afrika
Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
  • Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.