Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
Published: April 17, 2026 at 12:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32.

Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Yadda Aka Rarraba Kasafin Kuɗin 2026

A cikin wannan gagarumin kasafi na naira triliyan 68.32, an ware Naira triliyan 4.799 Domin ayyukan da doka ta tanada (Statutory Transfers), sai Naira triliyan 15.8 Domin biyan basussukan da ake bin ƙasa. Naira triliyan 15.4 Domin kuɗaɗen gudanarwa (Recurrent Expenditure), sai Naira triliyan 32.2 Domin ayyukan raya ƙasa (Capital Expenditure).

Wannan kasafi ya nuna cewa kusan kashi 50 cikin ɗari na kuɗaɗen za su tafi ne ga ayyukan raya ƙasa, wanda hakan ke nuna ƙudurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tattalin arziki, tsaro, da gina ababen more rayuwa ga ‘yan Najeriya.

Tsawaita Lokacin Kasafin 2025

Baya ga sabon kasafin, Shugaba Tinubu ya amince da gyaran dokar kasafin 2025 domin ba da damar ci gaba da amfani da kuɗaɗen ayyukan raya ƙasa har zuwa ƙarshen watan Yunin 2026.

Manufar wannan mataki ita ce tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) sun kammala manyan ayyukan da suke hannunsu ba tare da cikas ba, musamman waɗanda suka riga suka yi nisa.

Umarni Zuwa Ga Ma’aikatu

Shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen cikin gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowace kwabo ta yi amfanin da aka nufa don amfanin talaka.

Haka kuma, ya jinjina wa shugabanni da mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa bisa jajircewa da kishin ƙasa da suka nuna wajen hanzarta duba tare da amincewa da wannan kasafi.

A ƙarshe, Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a ɓangaren tattalin arziki don samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan Labarai
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027 Shirye-Shirye
  • Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu Najeriya
  • Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.