Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
Published: April 17, 2026 at 12:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32.

Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.

Yadda Aka Rarraba Kasafin Kuɗin 2026

A cikin wannan gagarumin kasafi na naira triliyan 68.32, an ware Naira triliyan 4.799 Domin ayyukan da doka ta tanada (Statutory Transfers), sai Naira triliyan 15.8 Domin biyan basussukan da ake bin ƙasa. Naira triliyan 15.4 Domin kuɗaɗen gudanarwa (Recurrent Expenditure), sai Naira triliyan 32.2 Domin ayyukan raya ƙasa (Capital Expenditure).

Wannan kasafi ya nuna cewa kusan kashi 50 cikin ɗari na kuɗaɗen za su tafi ne ga ayyukan raya ƙasa, wanda hakan ke nuna ƙudurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tattalin arziki, tsaro, da gina ababen more rayuwa ga ‘yan Najeriya.

Tsawaita Lokacin Kasafin 2025

Baya ga sabon kasafin, Shugaba Tinubu ya amince da gyaran dokar kasafin 2025 domin ba da damar ci gaba da amfani da kuɗaɗen ayyukan raya ƙasa har zuwa ƙarshen watan Yunin 2026.

Manufar wannan mataki ita ce tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) sun kammala manyan ayyukan da suke hannunsu ba tare da cikas ba, musamman waɗanda suka riga suka yi nisa.

Umarni Zuwa Ga Ma’aikatu

Shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen cikin gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowace kwabo ta yi amfanin da aka nufa don amfanin talaka.

Haka kuma, ya jinjina wa shugabanni da mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa bisa jajircewa da kishin ƙasa da suka nuna wajen hanzarta duba tare da amincewa da wannan kasafi.

A ƙarshe, Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a ɓangaren tattalin arziki don samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
Next Post: Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.