Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da kasafin kuɗin shekarar 2026, wanda jimillar kuɗaɗen da za a kashe a cikinsa suka kai naira triliyan 68.32.
Haka kuma, Shugaban ya sanya hannu kan dokar tsawaita lokacin aiwatar da ayyukan babban birnin na kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris, 2026, zuwa 30 ga watan Yuni, 2026.
Yadda Aka Rarraba Kasafin Kuɗin 2026
A cikin wannan gagarumin kasafi na naira triliyan 68.32, an ware Naira triliyan 4.799 Domin ayyukan da doka ta tanada (Statutory Transfers), sai Naira triliyan 15.8 Domin biyan basussukan da ake bin ƙasa. Naira triliyan 15.4 Domin kuɗaɗen gudanarwa (Recurrent Expenditure), sai Naira triliyan 32.2 Domin ayyukan raya ƙasa (Capital Expenditure).
Wannan kasafi ya nuna cewa kusan kashi 50 cikin ɗari na kuɗaɗen za su tafi ne ga ayyukan raya ƙasa, wanda hakan ke nuna ƙudurin gwamnatin Tinubu na ƙarfafa tattalin arziki, tsaro, da gina ababen more rayuwa ga ‘yan Najeriya.
Tsawaita Lokacin Kasafin 2025
Baya ga sabon kasafin, Shugaba Tinubu ya amince da gyaran dokar kasafin 2025 domin ba da damar ci gaba da amfani da kuɗaɗen ayyukan raya ƙasa har zuwa ƙarshen watan Yunin 2026.
Manufar wannan mataki ita ce tabbatar da cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati (MDAs) sun kammala manyan ayyukan da suke hannunsu ba tare da cikas ba, musamman waɗanda suka riga suka yi nisa.
Umarni Zuwa Ga Ma’aikatu
Shugaba Tinubu ya bayar da umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen cikin gaskiya da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowace kwabo ta yi amfanin da aka nufa don amfanin talaka.
Haka kuma, ya jinjina wa shugabanni da mambobin Majalisar Dokoki ta Ƙasa bisa jajircewa da kishin ƙasa da suka nuna wajen hanzarta duba tare da amincewa da wannan kasafi.
A ƙarshe, Shugaban ya sake tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da yin gyare-gyare a ɓangaren tattalin arziki don samar da ayyukan yi da inganta rayuwar al’umma.


