Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci
Published: April 22, 2026 at 2:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A wani gagarumin mataki na zamanantar da aikin dan sanda da rage radadin tsadar man fetur, Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta mika wa Rundunar ’Yan Sandan Najeriya (NPF) wasu manyan motocin bas guda uku masu amfani da iskar gas (CNG).

Wannan tallafi, wanda ya fito ne ta hannun Asusun Tallafawa ’Yan Sanda (NPF-TF) da kuma Kwamitin Shugaban Kasa kan Motocin Gas da Lantarki (PI-CNG & EV), an mika shi ne a ranar Laraba a helkwatar rundunar da ke Abuja.

Sufeto Janar na ’Yan Sanda, IGP Olatunji Rilwan Disu, ya bayyana jin dadinsa ga wannan hangen nesa na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa, Wannan canji zuwa amfani da makamashin gas da lantarki wani muhimmin mataki ne da zai sanya aikin dan sandan Najeriya ya tafi daidai da yadda ake yi a kasashen da suka ci gaba.

“Za a yi amfani da wadannan motoci ne domin inganta walwalar jami’ai da kuma saukaka zirga-zirgarsu yayin gudanar da ayyukan tsaro.” Inji shi.

Rundunar tana shirin samar da cibiyoyin canza fasalin motoci (conversion centres) a cikin gida domin su rika gyara da kuma kula da motocin da kansu.

Shugabannin hukumomin biyu, a karkashin jagorancin Sakataren NPF-TF, Mohammad Sheidu, da Shugaban PI-CNG & EV, Barista Ismail Ahmed (OON), sun tabbatar da cewa wannan somin-tabi ne.

“Wannan mataki na daya ne daga cikin babban shirin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin dukkan motocin aiki na ’yan sanda zuwa masu amfani da iskar gas (CNG). Wannan zai rage kudin da ake kashewa wajen sayen man fetur da kusan kashi 50% ko fiye da hakan.”

Taron ya samu halartar manyan jami’ai daga hukumomin biyu, ciki har da CP Tony Emafale, Alhaji Sanusi Aliyu, da sauran wakilai daga bangaren kwamitin CNG na fadar shugaban kasa.

Wannan hadin gwiwa wata hujja ce dake nuna yadda Gwamnatin Tarayya take jajircewa wajen samar da ingantattun kayan aiki ga hukumomin tsaro ta hanyar amfani da fasahar zamani mai rahusa kuma marar illa ga muhalli.

Matakin zai kara wa rundunar karsashi wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya a wannan sabon zamani.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki
Next Post: Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu

Karin Labarai Masu Alaka

FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Nnamdi Kanu Ya Nemi A Mayar Da Shi Abuja Daga Gidan Yarin Sokoto Labarai
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Amurka Tana Cigaba Da Kare Jami’in Da Ya Kashe Ba Amurke Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.